MARABA DA ZUWA SHAFINMU NA MUSULUNCI

31 Dec 2007

TARE DA MANZAN ALLAH SALLALLAHU ALAIHI WASALLAM NA (1)

HAIHUWAR MANZAN ALLAH SALLALLAHU ALAIHI WASALLAM

1. Allah Madaukakin Sarki Yace:. ( Hakika Allah yayi baiwa akan Muminai da ya aiko da manzo daga cikinsu, yana karanta masu Ayoyinsa, kuma yana tsarkakesu, kuma yana karantar dasu Littafi -wato Alk'ur'ani da Hikma -watom Hadisi, duk da sun kasance kafin hakan suna cikin bata a bayyane) S. Al'imaran-164.

2. kuma madaukakin Sarki yace: ( kace masu nifa mutum ne kamanku, anayimini wahayi cewa tabbas mahaliccinku shine ubangiji guda daya) S. kahf-11.

3. An tambayi Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam gameda Yin Azumin Ranar Litinin?

Yace: " wannan rana ce da'aka haifeni a cikinta, kuma a cikinta aka aikoni, kuma a cikinta aka saukar min da Alk'ur'ani" Muslim

4. Hakika an haifi Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam a Ranar Litinin cikin watan Rabi'ul Awwal a Makka, a shekaran Fil- wato Giwa. shekara ta 571 C.E. daga Iyaye biyu sanannu: Mahaifinsa shine ABDULLAHI dan Abdulmutallib, Mahaifiyarsa kuma itace AMINA yar Wahabu, kakansa yarada masa suna MUHAMMAD Sallallahu Alaihi Wasallam, kuma Mahaifinsa ya rasu kafin Haihuwarsa.

5. Lallai Yana daga cikin Abubuwan dasuke wajibi akan Musulmai shine su san darajan wannan Manzo me girma, kuma suyi hukunci da Alkur'ani da'aka saukar masa, kuma su dabi'antu da halayensa kuma su bada kokari wajen kira zuwaga Tauhidi-kadaita Allah- wanda akansa yafara...........................me bin Umarnin Allah Madaukakin Sarki: ( Kace ina kira zuwaga Ubangijina kuma bazana hadashi da kowa ba cikin bauta). Sur.Aljinn-20.

18 Dec 2007

LAYYA

16 Dec 2007

YANKAN LAYYA BA'A GARIN ME LAYYA BA

TAMBAYA: Mu muna zaune a wani Gari, kuma Mahaifiyata da Y'an Uwana suna yanka wani adadi na Layya a kowace shekara, Ni kuma inaso in aikawa da Kawuna da kudin abin Layya na , don yasaya yayi min yankan, saboda halin talauci da suke a ciki, kuma shi kawuna yana zaune a wani gari ne da ban, shin ko zaku bani shawara gameda haka, koko inyi layya na a garin danake zaune, kuma wanne ne yafi falala? tunda ni zan wakilta wani ne da yayi min yankan, kuma bazanga dabban ba yayin da'ake yankata. MAI BADA AMSA: Prof. Dr. Sa'ud bn Abdullah Alfunaisan. Tsohon shugaban Faculty of Shari'ah, Imam Muhammad Bn Sa'ud University Riyadh. RANA: 05-12-1428 A.H. AMSA: Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah, Tsira da Aminci su Kara tabbata ga Manzan Allah. Bayan Haka: Ya Halarta ka wakilta Kawun ka dayake wani gari da kabashi kudin yasaya kuma yayi maka yanka, saboda ita dai Layya, sunna ce me karfi, wasu kuma sukace wajibi ce ga wanda yake da hali, kuma kallon yankan da kuma cin naman abin layyan, sunna ce ba wajibi ba, musamman kuma tunda Iyalanka zasu yi layyan, kuma abin layya guda daya yana isarma mutum da iyalan gidansa koda suna da yawa, kuma kamar yadda ka bayi bayanin halin da kawunka yake ciki wato yafi iyalanka bukata, saboda haka inka bashi kudin layyan yana wata kasa yayi maka, yahalarta a cikin Shari'a. Allah shine mafi sani.

11 Dec 2007

HAJJI DAI FARKO

Ni Babban ma'aikaci ne kuma me tarbiyya, Alhamdu Lillah Bani da gidana nakaina, ina haya ne, kuma ina da kudin da baze isheni sayen gida ba amma ze ishe ni yin aikin Hajji. shin zan sauke faralin Hajji ne tareda cewa ina haya? shin kuma ya halarta agareni da in jinkirta yin Hajjin har se nase gida, tare da cewa wannan hakan ze dauki shekaru masu yawa? Daga: Shafin: www.islamtoday.com/questions Malami me Amsa: Al'allama Ustaz Dr. Abdullahi bn mahfuuz bn biih, tsohon Ministan ma'aikatan Shari'a ta kasar Mauritania. Rana: 01-12-1428 A.H. Amsa: Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah, Tsira da aminci su tabbata ga Manzan Allah. bayan haka Wajibine gareka yakai dan'uwa da kaga batar da wajabcin Hajji, domin shi wajibine da baayin jinkiri a cikinsa, kamar yanda da yawa daga cikin Malamai suka tafi akai, to tunda kanada kudi daze ishekan yin aikin Hajji, kuma bazaka bar iyalanka ba a cikin kunci, toyazama dole akanka katafi kayi aikin Hajji kada ka jinkirta shi, domin Hajji wajibi ne, wanda ba'a jinkirta shi, kasmar yanda Imamu Malik da Imamu Ahmad suka tafi akan haka, kuma zance ne me k'arfi a wajen Hanafiyya.

9 Dec 2007

SUMBANTAN KA'ABA?

DAGA: Shafin: www.meshkat.net TAMBAYA: Shin Yana daga cikin Sunnah Sumbantan Ka'aba? MAI BADA AMSA: Sheikh Dr. Abdul-Hayyi Yusuf. Limamin Masallacin Jum'a dake Hayyud dauha, a Khartoum kuma Shugaban Sashin Thaqaful-Islamiyyah a Khartoum University a kasar Sudan. Dukkan Godiya ta tabbata ga Allah Shi kad'ai, kuma Tsira da Amincin Allah su kara tabbata ga wanda babu wani Annabi a bayansa, da Alayensa da Sahabbansa baki daya. Bayan Haka: Abinda yake Sunna dai, Shine sumbantan Hajarul Aswad da Ruknul Yamaani, kuma baya daga cikin Sunnah sumbantan wani abu wanda ba su ba, kamar ka'aba Allah yakara mata, kuma Sahabi Abdullahi dan Abbas Allah yakara masa Yarda, yayi inkari - wato ya nuna kyamarsa ga wanda ya sumbanci wani abu wanda ba Ruknai guda biyu ba- wato wanda aka ambanta-. Allah shine mafi sani.

29 Nov 2007

ABUBUWAN HANI A CIKIN HAJJI

ABUBUWAN DA AKA HARAMTASU GA MAHAJJACI

Duk wanda yayi Harama da Hajji ko Umurah an haramta masa, abubuwan da suke zuwa: 1.Rufe kai ga na miji, domin haramarsa itace bude kai, haka kuma Rufe fuska da Hannaye ga mace, domin haramarta itace budesu, sedai idan zata wuce maza, to seta rufe fuska. Kuma idan daya daga cikinsu yarasu, to za’a rufeshi a cikin haraminsa, se abude fuskar maace, kuma a bude kan na miji, kuma baza’a samasa turare ba.

2. Aske gashin kai ga na miji.

3.Yanke kumba.

4. Sanya Turare, sedai abinda yake a tufafinsa, wanda yayi harami dashi to babu laifi akansa.

5.Sanya tufafi dunkakke.

6. yin Jima’I da abubuwan dasuke haifar dayinsa.

7. Yin farautan wani abu, ko temaka ma meyin hakan, ko cin abinda akayi farautarsa.

8. Yayi tad’i wato neman aure, ko daura masa aure, ko aurarwa waninsa, ko ya halarci daurin auren waninsa.

WAR-WARE AIKIN HAJJI KARAMA DA BABBA

Mahajjaci yanada war-wara guda biyu: Karama shine bayan jifan jamratul ak’aba –wato shedan babba- a ranar Idi kenan, to daga nan komai ya halatta ga mahajjaci hatta saduwa da Iyali. da kuma War-wara babba, wanda yake bayan dawafin Ifada.

FIDIYA GA WANDA YA AIKATA ABINDA AKA HARAMTA

Duk wanda ya aikata daya daga cikin abubuwa guda biyar na farko da’aka haramta masa, da gangan –wato-yana sane bada mantuwa ba- to akwai fidiya akansa, kuma yanada zabi a cikin hakan, kodai ya yanka dabba, ko ya ciyarda Miskinai guda shida, ko yayi Azumin kwana uku (3) a duk inda yaso. Saboda faden Manzan Allah Sallalahu Alaihi Wasallam ga Ka’ab dan Ujratu Allah yakara masa yarda: …………………………………………………

AIKIN HAJJI

Menene Ma'anar Hajji? Hajji a harshen larabci ma'anarsa itace nufi ko aiki da yake zuwa lokaci zuwa lokaci. Amma a musulunci, idan akace hajji shine Nufin dakin Allah me alfarma domin aiwatar da wasu ayyuka kebantattu da Alalh madaukakin sarki ya ambata acikin littafinsa kuma Hadisai sukayi bayani akansu.

HUKUNCIN AIKIN HAJJI

Yin aikinHajji wajibine akan kowani musulmi na miji da musulma mace dasuke da iko. Kuma aikin Hajji ya tabbata acikin Littafi da Hadisi da Ijma'i.

Daga cikin Littafi : Allah madaukakin Sarki Yace: ( kuma lallai Allah ya wajabta wa mutane yin Hajjin dakinsa ga wanda yasami iko,kuma duk wanda ya kafirce to lallai Allah mawadaci ne ga Halittu.) Sur. Al'imrana

Daga Hadisi : Abdullahi dan Umar ya ruwaito Hadisi daga Mnazan ALLAH Sallalllahu Alaihi Wasallam yace: ( An gina musulunci ne akan abubuwa guda biyar : Shaidawa babu abin bautawa da can canta se Allah kuma Annabi Muhammadu Manzan Allah ne,Tsayar da Sllah, Bayar da Zakkah, Yin Hajji da kuma Azumin Watan Ramadana) Bukhari da muslim.

Daga Ijmaa'I : Dukkan Musulmai sun hadu akan wajabcinshi kuma dayane daga cikin rukunnan musulunci, kuma abune da kowa yasanshi acikin Addini, kuma duk wanda yyi musunsa to ya kafirta kuma yaayi rudda daga musulunci, haka kuma malamai sun hadu akan cewa aikin Hajji baya wajaba face sau d'aya a rayuwar mutum se dai idan mutum musulmi yayi bakancensa wato alwashi to yazama dole ya cika alwashinsa, amma duk abinda yayi bayan wannan to neman lada ne kawai.

Abdullhi dan Abbabs Allah yakara yarda agareshi yace Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yayi mana Khud'uba, se yace: (Yaku mautane Allah ya wajabta aikin Hajji akanku ) se Ak'ra'a bin Habis yace "Shin kowace shekarane ya manzan Allah? Se yayi shiru har se da ya maiamaita hakan sau Uku, sannan Manzan Allah Sallallahu Alaihin Wasalllam yace : ( da'ace nace E da yazama wajibi, kuma da dayazama wajibi bazaku yiba kuma bazku iyaba, Hajji sau dayane duk wanda yakara to neman ladane ) Ahmad, Abu dawud da Nasa'i.

FALALAR AIKIN HAJJI

Allah ya kwadaitar damu yin aikin hajji kuma ya bayyana d'umbin ladar da za'a samu a sakamakon hakan hadisan dasuke zuwa zasu bayyana haka:

Fadin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam : ( Duk wanda yayi Hajji, be yi rafasu ba -wato Jima'i a cikinsaba- kuma beyi fasikanciba –sab'on Allah- ze koma mara laifi kamar randa mahaifiyarsa ta haifeshi ) Bukhari da Muslim.

Fadin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam : (Yin aikin Umurah zuwa Umurah ana kankare zunubbai dake tsakaninsu, shiko aikin Hajji karbabbe baya da sakamako se Aljanna.) Bukhari da muslim.

Fadin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam : yayinda aka tambayeshi gameda mafificin ayyuka se yace " Imani da Allah da manzansa" akace seme kuma? Yace "se jihadi dan daukaka kalmar Allah" akace se me kuma? Yace" se aikin Hajji karbabbe". Bukhari da Muslim.

Fadin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam………………..

SHARUDDAN WAJABCIN HAJJI

Seda sharudda masu zuwa hajji yake zama wajibi:

1. Musulunci

2. Balaga

3. Hankali: wato yakasance me hankali domin Hajji baya wajaba akan mahaukaci.

4. Y'anci: wato yazama d'a,domin hajji baya zama wajibi akan bawa. Dalilan wadannan sun gabata a cikin rukunin Azumi.

5. Samun iko: kamar yadda Allah madaukakin Sarki yace ( kuma lallai Allah ya wajabta wa mutane yin Hajjin dakinsa ga wanda yasami iko….) Sur. al'imrana -97.

RUKUNNAN HAJJI

Rukunnan Hajji guda hudune(4): Yin harama, Tsayuwa a Arafah, Yin d'awafi da Yin Sa'ayi kuma rashin yin daya daga cikin wadannan yana bata hajji.

Na Farko: Yin Harama: shine Niyyan shiga cikin aikin hajji ko Umurah kuma niyyan takasance a ntareda lokacin da mutum ze cire tufafinsa da talbiyya. Kuma harama tana da nau'o'i uku: Tamattu'I, Qiraani da Ifraadi.

Tamattu'I : ma'anarsa shine musulmi yayi harama da Umara ita kadai a cikin watannain Hajji, idan ya 'isa makka se yayi dawafi yayi sa'ayin umura yayi k'wal kwabo ko saisaye, idan ranar tarwiya wato ranar takwas ga zulhajji, se yayi harama da Hajji shi kad'ai yayi dukkan ayyukan Hajji ya yi hadayan Tamattu'I da yayi idan shi ba mazaunin garin makka ne ba.

Qiiraani: shine yayi harama da Umara da Hajji a tare daga mikaati ko kuma yayi harama da Umara a farko se yashigar da aikin hajji a ciki kafin yayi dawafi kuma ze cigaba da kasancewa a cikin haraminsa har zuwa lokacin da zeyi jifan jamrah a ranar idi se ya aske kansa kuma yayi hadaya kamar me tamattu'i.

Ifraadi : shine yayi harama da hajji kadai, ya cigaba da zama a cikin haraminsa har zuwa lokacin da ze jefi jamrah ranar idi sannan ya aske kansa kuma babu fidya akansa wato babu jini akan haka.

28 Nov 2007

FATAWA AKAN MAFARKI (2)

DAGA: Shafin: www.islamtoday.com Menene Bambanci tsakanin Wankan Janaba da Wankan tsabta? wajen isarwarsu daga alwala ko rashinta? kuma shin yin Alwala sharadi ce gameda wankan tsabta? dakuma wajen yin niyya, Allah yasaka maku da Alkhairi. Mai bada Amsa: Dr. Sulaiman bin Wa'il Attuwaijiri, Mamba a kwamitin malamai na Jami'ar Ummul Qura dake makkah. Rana: 27-6-1424 A.H. Amsa: Wankan Janaba, wankane dayake dauke Hadasi babba, ita kuma Alwala tana dauke hadasi ne wanda yake karami, shi kuma wanka na tsabta, ba ya dauke wani hadasi, to da mutum zeyi niyyan wanka, wato bana janaba ba, kawai yayi wankan tsabta ne ko wankan juma'a, se yayi nufin dauke hadasi karami dashi wato alwala, to be isar masa ba, domin a wankan babu nufin dauke hadasi a cikinsa, Allah madaukakin Sarki kuma yana cewa "kuma idan kun kasance masu janaba to kuyi tsarki" to alwala tana shiga cikin wankan janaba wajen dauke hadasi, se hadasi karani ya shiga cikin hadasi babba, wajen daukewa da abinda ze halarta sallah, amma shi kuma wanka na tsabta, badauke hadasi yakeyi ba saboda haka be idarwa gameda alwala, myazama dole yayi alwala da farillanta da jerantawa a gabbai. Allah dhine mafi sani.

FATAWA AKAN MAFARKI (1)

Menene Ma'anar Mafarki kuma Yaya Yake? Daga Shafin: www.islamtoday.net/question Mai Amsa Tambaya: Al-allamah Abdurrahman bn Abdullahi Al-ajlan Malami a haramin Makkah. Rana: 15-12-1422 A.H Amsa: Mafarki Shine mutum yagansa yanayin Jima'i da wata mace, to idan ya fitar da maniyyi a wannan lokaci to wanka ya wajaba akansa, idan kuma bai fitar da maniyyi ba, wankan bezama dole akansa ba, saboda fadin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam "Ruwa yana wajaba ne -wato yin wankan janaba- saboda fitar ruwa -wato maniyyi" Muslim ya ruwaitoshi lambar hadisi na 343 daga hadisin Abu Sa'idil Khuduri Allah yakara masa Yarda.

27 Nov 2007

FATAWA AKAN TABARRUKI

Menene Hukuncin Tabarruki (Neman Albarka) da duk wani abu da yashafi Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam, a Lokacin dayake da rai, da bayan mutuwarsa, da tabarrukin da Sahabbai sukayi da Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam a lokacin rayuwarsa, kuma shin hakan ya tabbata a bayan rasuwarsa? kuma naji cewa Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yaba wani bargonsa, kuma a binne wani dashi a bayan mutuwarsa? kuma shin yatabata cewa Abdullahi dan Umar yayi tabarruki da mimbarin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam? kuma meye ra'ayinku gameda wanda yake cewa yanada gashin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam?.
Malami da ya amsa: Ustaz Dr. Khalid almushaiqih
Rana: Alhamis 30 Rajab 1427 A.H
Lambar Fatawa: 16619.
Daga: shafin www.almoslim.net
Dukkan yabo da godiya sun tabata ga Allah Mahaliccin Bayi, tsira da Amincin Allah su tabbata ga Annabi Muhammad da Alayensa da Sahabansa gabaki daya. bayan haka:
Yin Tabarruki da Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam a lokacin da yake da rai, ya kunshi nau'i guda biyu na Albarka, Albarka tashi da kansa da Albarka ta ma'ana.
Amma neman albarka tashi ta kansa: To Sahabai Allah yakara Yarda agaresu, sun kasance suna yin tabarruki da Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam, saboda Allah Subhanahu Wata'ala yasanya albarka agaresa, kamar yanda hakan yazo a cikin Hadisin Bukhari da Muslim da waninsu, cewa sunayin tabarruki da Gashinsa da Yawunsa da kakinsa da guminsa da tufafinsa da sauransu. Nau'i na biyu kuma shine: yin Tabarruki na Ma'ana, Annabai Sallallahu Alaihi Wasalllam, Shine mafi girman dalili ko sababi ga al'ummarsa na samun Albarka ta hanyar karantarda su da shiryar dasu da fitar dasu daga duhu zuwa gas haske. to amma bayan wafatinsa, to Albarka ta ma'ana ta yanke, sedai abinda aka ruwaito daga wasu daga cikin Sahabbai Allah yakara masu yarda, cewa sun kasance sun kiyaye wasu daga cikin abubuwa na Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam kuma sunayin Tabarruki dasu kamar yadda yazo a cikin Sahih Abukhari, daga Ummu Salamah Allah yakara yarda agareta, tanada abun wuya na azurfa ta kiyaye gashin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam a ciki, to irin wadannan alamomi ko abubuwa, sahabbai sun kasance, sun kiyiyesu. To amma a Yau: irin abinda shuwagabannin Sufaye suke ik'irari da y'an damfara na cewa sunanan da wani sashi na gashin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam, ko tufafinsa ko makamancin haka, duk k'arerayine da basu da wata kamshin gaskiya, saboda basu da wani dalili -wato hujja akan hakan- ingantatta a cikin Shari'a ta sanadi, to saboda haka babu wani abinda yarage face, Albarka ta ma'ana, ta neman Albarka da abubuwan daya fuskantar, da abubuwan dayayi umarni dasu da abubuwan dayayi hani dasu da tsayuwa akan Sunnarsa da nisantar Sab'a masa. kuma ga Allah muke neman dacewa.

1 Nov 2007

Jana'izar Malam Ja'afar

Wannan Itace Jana'izar Sheikh Ja'afar Mahmoud Adam Allah Yayi masa Rahama Amin.

29 Oct 2007

..... KE BATA ZUCIYA.....

Bismillahir Rahmanir Rahim
ABUBUWAN DA SUKE BATA ZUCIYA
Na: Imamu ibnul Qayyim
Imam ibnul Qayyim Allah yayi masa rahama yace: Amma abubuwan da suke bata zuciya guda biyar sune wanda yayi nuni akansu: yawan Cakud’a da mutane, da buri, da rataya da wani wanda ba Allah ba, da K’oshi, da barci. Wadannan sune manyan abubuwa guda biyar da suke bata zuciya.
NA FARKO: YAWAN CAKUDA DA MUTANE: Amma tasirin da yawan cakuda da jama’a yakeyi shine Zuciya zata cika da da Hyakin Numfashin Yan Adam har tayi bak’i, kuma hakan ze tilasta masa darewa da rabuwa da damuwa da bakin ciki,da rauni, da daukan abinda baze iya daukansa ba na takaicin Abokan banza, da bata abubuwan da zasu kawo masa amfani, da rafkana wato shagaltuwa daga barinsu, da wadansu al’amura, da kuma rarraba tunaninsa wajen nufinsu da nemansu, To menene yarage a wurinsa na ALLAH da ranar lahira?
* Wannan kenan, kuma dayawa daga cikin cakuda da mutane ya jawo bala’i, kuma yazama sanadin hana samun ni’ima, da saukar da Jarrabawa, da lalacewar dama, da musiba ta fad’o, kuma da aukuwan bala’i, kuma shin ba duk cutarwan dayake samun mutane ba, mutane ke zama sanadi?
* Kuma wannan cakuda da jama’an yana kasancewa ne wani nau’i ne na soyayya anan duniya, amma ze juye yazama Hukunci da gudun sashinsu daga sashi, idan kiyayya ta gaskiya ta tabbata, kuma me cakuda da jama’a ze cizi yatsa saboda nadama, kamar yanda Allah madaukakn Sarki yace: (“kuma a ranar da me zalunci yakeyin cizo akan hannayensa, yana me cewa: kaicona Inama da ace nabi tafarkin manzo! Ya kaicona! Inama! da ace ban riki wani masoyi ba! Tabbas, Hakika ya batar dani bayan tunatarwa tazo mini, kuma lallai Shed’an ya kasance ga mutum me zumbulewa.” Sur.Furqan 27-29) kuma madaukakin sarki yace: (Masoyan juna a wannan yinin, sashinsu mak’iyi ne ga sashe in banda masu tak’awa” (wato masu jin tsaoron Allah su masu san junane) Sur. zukhruf 67) kuma Badansa –wato Annabi Ibrahim- Yace: (“Babu abinda kukayi sedai kun riki gumaka saboda soyaiyar tsakaninku a cikin rayuwar duniya. Sa’an nan a ranar k’iyama sashinku ze kafirce ma sashi,kuma sashinku ze tsinewa (la’anta) sashi kuma makomarkun itace wuta, kuma Azzalumai basuda wadansu ma temaka” Sur. Ankabut 25)
* Kuma ma’auni me amfani a cikin cakudanya da jama’a: shine: yayi cakuda da mutane a cikin alkhairi, kamar Sallar juma’a da sallar Jam’i, da Iduka da Hajji, da koyan karatu da Jihadi, da yin Nasiha.
kuma ya kauracemasu a cikin aikata sharri, da halal din da baya da amfani.
* Idan bukata tasa shi haduwa da jama’a, ta yanda be sami daman kadaituwa daga garesu ba, to yaji tsoro kada ya goyi bayansu, kuma yayi hakuri akan cutarwan su, domin dole su cutar dashi, matukar beda karfi ko matemaki.
Sedai cutarwa ne da daukaka zata biyo bayansa, da soyayya agareshi, da girmamawa da yin yabo agareshi, daga wajen muminai da ubangijin halittu, kuma goyon bayansu kaskancine zebiyo bayansa da kiyyaiya gareshi, da Fushi da zargi daga wajensu, da muminai, daga ubangijin halittu. Saboda haka yin hakuri akan cutarwansu shine yafi alkhairi kuma yafi makoma me kyau, kuma yafi godiyan makoma.
* Kuma idan bukata tasa ya cakudu dasu a ckin halal da bashi da amfani, se yayi kokari ya juya wannan zaman yakoma yin biyyaiya ga ALLAH idan yasami dama.
NA BIYU: HAWA KAN TEKUN BURACE-BURACE:
Kuma shi kogine da beda tudu. Shi rafine wanda marasa rabo ke hawa daga cikin halittu, kaman yanda aka ce: guguwan burace – buracen karya, da tunanin banza, bazata gusheba, tana wasa da wanda ya hauta, kamar yadda karnuka ke wasa da gawan mamaci, kuma kaya ce na kowace rai, wulakantacciya kaskantacciya dake kasa, batada himman da za’a sami gaskiya da ita a fili, kai tasaba da burace –buracen kwakwalwa. Kuma kowanne da irin halinsa: daga me burin abin koyi da sarauta, da kuma Fatauci abayan kasa da zagaye – zagayen garuruwa, ko saboda dukiya da kudi, ko dan mata da yan samari, wanda yakeda burace – burace yana kama da wata sura da yake nema a cikin zuciyarsa wanda yasami rabo da samunsa, kuma yaji dadin samu rabo dashi, to yayin da yake a ckin wannan yanayi, se kawai yafarka se gashi akan tabarma!!
*To me himma datake babba, burace – buracensa sunna kewayawa ne a tsakanin da Ilimi da Imani, da yin aikin daze kusantashi zuwa ga Allah (Ubangijinsa) kuma ya matsar dashi zuwaga yin makwabtaka dashi. To burace – buracen wannan shine Imani da haske da hikma, amma burace –buracen wadancan zambace da rudu.
Kuma hakika manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yayi yabo akan masu yin buri na alkhairi, har ma yasanya ladan wanda yayin burin aikata aikin alkhairi kamar na wanda ya aikata din.
NA UKU: RATAYUWA DA WANDA BA ALLAH BA MADAUKAKIN SARKI: Kuma Wannan shine mafi girman abinda ke bata zuciaya kai tsaye, bashi da abinda yafi wannan cutarwa, kuma abinda yafi wannan yanke masa abubuwa masu amfani da tsira kamansa,domin idan har yaratayu da wanda ba Allah ba, Allah se ya dogarar dashi zuwa ga wannan abinda daya ratayu dashi, mutuwansa yasami abinda yakeso a wajen wanda ba Allah ba daya Ratayu dashi, da juyawarsa zuwa ga waninsa, shi din be sami rabonsa da yake wajen Allah ba, kuma be kai wajen abinda yake buri ba, da ya ratayu dashi. Allah madaukakin Sarki yace: (“kuma sun riki wadanda ba Allah ba (wato gumaka) a matsayin abin bauta don suzama matemaka a garesu, A’aha zasu kafircema ibadarsu, kuma su kasance mak’iya akansu” Sur. maryam 81 -82) kuma yace: (kuma sun riki wadansu abubuwan bautawa da ba Allah ba, sunyi tsammanin zasu temakesu. ( Bazasu taba iya temakonsu ba, alhali su din runduna ce daza’ akawosu (cikin wuta) Sur. Yasin 74 -75).
* Wanda yafi kowa kaskanci: shine wanda ya ratayu da wanda ba Allah ba, domi duk abinda yawuceshi na maslahohinsa da tsiransa da samun rabonsa, shine mafi girman abinda yasamu daga wanda ya rtayu dashi, shi yana fuskantar gushewa da kufcewa.
Kuma misalin wanda ya ratayu da wanda ba Allah kamar kwatankwacin wanda yake neman Inuwane daga zafi ko neman sanyi agidan gizo – gizo, mafi raunin gidaje.
* A dunkule: tushen shirka da K’a’idar da aka ginashi akanta: shine ratayuwa da waninda ba Allah ba. Kuma me yin hakan abin zargine kuma abin kaskanci, Allah madaukakin sarki yace: (“kada ka hada wani da Allah a wajen bauta, har kazauna kana abin zargi wulak’antacce” Sur. Isra’i -22) ma'anan abin zargi: bakada me gode maka, wulakantacce: kuma babu me temako agareka.
NA HUDU: ABINCI: Kuma abinci yana bata zuciya ta nau’i biyu:
Na d’aya: abinda ke bata zuciyan dakansa sune kaman abubuwan da’aka haramta. Kuma suma sun kasu kashi biyu: * Abubuwan da’aka haramta saboda Allah, kamar mushe, da Jini, danaman kare, da masuyatsu daga cikin dabbobi, da tsuntsaye masu k’unba. * Abubuwan da’aka haramta saboda bayi: kamar abinda aka sata,da wanda akayi kwacensa, da wanda akayi fashinsa, da duk wani abinda aka amsa a hannun meshi ba tareda izininsa ba, kodai fin karfi kokuma jin kunya da zargi.
Na biyu: Abinda ke bata wani sashi na zuciya kuma yawuce iyaka, kamar yin almubazaranci da abinda yake halal ne, da koshi wanda yawuce iyaka, domin ze hanashi yin abubuwan d’a a (biyaiya), kuma ya shagaltar dashi da cin abincin daze cika mai ciki sosai, yin kokari har se yasami hakan, kuma idan yasameshi, to ze hanashi (gudanarda hakan?) wato zesashi tumbi-da yin kariya daga abinda ze cutardashi, da cutuwa da nauyinsa, kuma abubuwan da sukesa sha’awa zasu yi k’arfi agareshi, kuma zebi hanyar shedan ya fadadata, domin yana gudu a jikin dan Adam kamar yadda jini ke gudu (yana bin hanyar jini ajikin dan adam). To Azumi kuma yana kuntatasu kuma ya yoshe hanyoyinsa, kuma duk wanda yaci abinci da yawa to ze sha ruwa da yawa, kuma zeyi barci me yawa kuma yayi asara me yawa. Kuma yazo cikin hadisi mashhuri: (“Dan Adam be cika mazubinsa- tumbinsa ba- da sharri fiyeda cikinsa, wasu y'an lomomi sun isa dan Adam wanda ze tsayu da doronsa ko bayansa. Idan kuma yakasance babu makawa, to daya bisa uku na abincinsa, daya bisa uku na abin shansa,daya bisa uku na numfashinsa,” Tirmidhi da Ahmad da Hakim)
NA BIYAR: YAWAN BARCI: Domin kashe zuciya,kuma yasa jiki yayi nauyi, kuma ya bata lokaci,kua nya gadar da yawan mantuwa, da kasala.
Kuma daga cikin barcin akwai wanda yake makaruhi ne (abinda aka kyamaci aikatashi) daga ciki akwai wanda yake cutarwa, wanda beda amfani da yake cutarda jiki, kuma barci mafi amfani: shine wanda akayishi lokacin tsananin bukatuwa zuwa gareshi. Da barcin Farkon dare, shine yafi amfani akan na karshensa,kuma barcin tsakiyar rana shi yafi amfani akan na farkonsa da na karshensa, kuma duk lokacin da barci yayi kusa da farkonsa ko karshensa, amfaninsa yana raguwa, kuma cutarwarsa yana karuwa, musamman ma dai barci da la’asar. Da barcin farkon rana sedai ga wanda beyi barci ba da daddare da yawa.
* Daga cikin makaruhinsa (barci) akwai: Yin barci tsakaicin sallar Asubahi da fitowar rana, domin lokacine da’ake samun Ganima (rabon arziki) kuma tafiya a wannan lokaci tanada fifiko me girma koda sun kasance sun kwana suna tafiya, ba'aso su tsaya a wannan lokacin har se rana ta fito, shine farkon Yini da mabudinsa, kuma lokacin saukowar arziki, da samun kaso, da saukar albarka. Kuma a cikinsa Yini ke farawa, kuma a lokacin ne ake janye hukuncin samun kason wannan yini. Saboda haka yakamata yin barci a cikinsa yazama ga wanda yazama masa dolene kawai wato kamar barcin wanda ya matsu.
* A dunkule matsakaicin barci da me anfaninsa shine,barcin a rabin lokacin dare na farko,da kuma karshensa, kuma shine kwatankwacin awa takwas. Kuma wannan shine mafi dacewar barci, kuma gwargwadan abinda ya karu akansa ko ya ragu, gwargwardan yadda zeyi tasiri a adabi’ance.
* Daga cikinsa akwai wanda beda amfani: shine yin barci a farkon dare, daf da faduwan rana har zuwa sanda duhun, Isha ze bace. Kuma Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yakasance yana kyamatarsa. To shi abin k’ine a shari’ance da kuma dabi’a. Allah ya temakemu.

6 Oct 2007

HUKUINCE HUKUNCEN SALLOLIN IDI (Karamar Sallah da Babba)ٍ

Dasunan Allah Mai Rahama Mai Jinkai

SALLOLIN IDI GUDA BIYU

Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya shar'anta ma bayinsa yin Iduka guga biyu, sallar Idi guda biyu, Sune Sallar Idi Karama da Idi Babba

HUKUNCIN YINSU

Halartar Sallar Idi dai Sunnah ce, wacce take mekarfi wato kamar wajibi take, saboda Allah madaukakin Sarki Yayi Umarni dasu inda Yace: (Lallai ne mu munyi maka kyauta mai yawa, saboda haka kayi Sallah domin Ubangijinka, kuma kayi suka –wato sukan rakumi ko yanka- kenan.) Sur, kauthar.1-2

Kuma ya rataya samun rabo da ita inda yace: (Hak'ik'a wanda ya tsarkaka (da imani) yasami babban rabo, kuma ya ambaci sunan ubangijinsa sannan yayi sallah.) Sur. A'ala 14-15

LOKUTAN YINSU

Shine lokacin da rana ta fito sama gwargwadon dagawan mashi daga k'asa har zuwa lokacin Gushewar rana (zawali) amma abinda akafiso shine ayi Idi babba a farkon lokaci, saboda mutane su samu daman yanka layyansu, Idi karama kuma anfiso a jinkirta ta saboda mutane su sami daman fitar da zakkan kono. Yatabbata manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Yana yin hakan a Hadisin Jundub Allah yakara yarda agareshi.

LADUBBANSU DA ABUBUWAN DA SUKE MUSTAHABBAI ACIKINSU

1. Yin Wanka da Sanya turare da Sanya mafi kyawun tufafi. Saboda fadin Anasa Allah Yakara Yarda Agareshi Yace: (Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Ya Umarci mu da mu sanya mafi sabunta abinda muka samu , kuma mu sanya mafi kyawun turare, kuma muyi layya da mafi tsada daga abinda muka samu-wato muke dashi) Imamul Hakim.

Tunatarwa: Amma ba'a sanya jajayen kaya biyu wato taguwa da wanda, ko me ruwan rawaya guda biyu, saboda manzan Allah ya hana sa wadannan launukan, amma babu laifi idan guda dayane

2.Cin Abinci kafin fita zuwa Sallar Idi K'arama, Ranar Idi Babba kuma se idan andawo daga Idi sannan se aci daga abin Layya, wato yanka da mutum yayi. Saboda Hadisin Buraidah Allahn Yakara masa Yarda Yace: (manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Yakasance Baya yin Sammako a Ranar Idi K'arama har se yaci, -wato se yaci wani abu- kuma bayaci a Ranar Idi Babba har se yadawo, se yaci daga abin Layyansa.) Imamut-Tirmidhi

3. Yin Kabbarori tun daga daren Idi Karama da Idi Babba, na Idi Karama za'a cigaba dayi lokacin fitowa daga gida zuwa filin Idi, baza'a yanke ba har se Liman Ya'iso, snnan a yanke. A idi Babba kuma za'a cigaba dayi har zuwa kwanaki uku na Shanyan Nama wato na Layya, Ga Lafazin Kabbarorin: Allahu Akbar Allahu Akbar La'ilaaha illallaah, Allahu Akbar Allahu Akbar, Walillaahil Hamd. Kuma an karfafa san yinsu a lokacin fitowa daga gida zuwa Filin Idi, da Bayan Sallolin Farilla guda biyar, a kwanakin Idi babba saboda fadinAllah Madaukakin Sarki: (kuma ku ambaci Allah a cikin wasu kwanaki k'ididdigaggu) Sur. Baqarah-203.

Da fadansa ( kuma ya ambaci sunan Ubangijinsa Kuma yayi Sallah)Sur. A'ala 15. da fadansa (..domin ku girmama Allah Saboda Shiriyar da yayi maku…) Sur. Alhajj-37.

4. Fita zuwa filin Sallar Idi ta wata Hanya da dawowa ta hanya ta dabam wato sauya hanya kenan Saboda manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Yakasance yana aikata hakan kamar yadda Jabir yafada acikin hadisi Allah Yakara masa yarda. Bukhari ya ruwaitoshi.

5. Yin Sallar Idi a fili, se dai idan an samu ruwan sama, ko makamancinsa to se ayi a cikin masallaci. hakan Yazo cikin Hadisi ingantacce.

6. Yima juna Barka ko Murna da Idi, da fadin: TAQABBALAL LAHU MINNA WA MINKUM saboda Sahabban Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam sun kasance in sun sauko Idi suna fadama junansu Haka idan suka hadu ( taqabbalal lahu minna wa minkum) Imamul Baihak'i. Ma'ana Allah Ya Karba Mana Idinmu tare danaku.

7. Rashin Yin Almubazzaranci a abinci da abin Sha, das wasa wanda aka halasta, saboda fadin manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam: ( Ranakun Idi ranaku ne na ci da sha, da ambaton Allah Madaukakin Sarki ) Imamu Ahmad.

SHIN KO ANA YIN NAFILA KAFIN IDI KO BAYANTA?

Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yayi hani da yin Salla kafin Idi ko Bayanta kuma ba'ayin kiran Sallar Idi ko tada Ik'ama, haka kuma Sahabbansa.

SAURAREN KHUDUBA

Anaso ga Wanda ya halarci Sallar Idi da yatsaya ya saurari Khuduba domin akwai lada acikin hakan, amma anyi rangwame ga wanda beso yaji da yatafi batareda yatsaya yayi surutu ga masu sauraro ba, kuma haka anyi rangwame ga wanda yayi Sallar Idi base ya halarci juma'a ba, wato idan Idi ta kasance ranar juma'a kenan.

Ya Allah ka sanya ayyukanmu suzama saboda kai kuma ka karba manasu Amin.

4 Oct 2007

Yin Azumin Sittu Shawwal

Azumin Sittu Shawwal

Imamu Muslim ya fitar da Hadisi ingantacce Daga Abu Ayyub Al'ansari Allah Yakara Yarda agareshi daga ManzanAllah Sallallahu Alaihi Wasallam Yace: (Duk Wanda ya Azumci Ramadan Sannan Y bishi da Azumi Shida a cikin Shawwal ya kasance kamar wanda ya Azumci shekara) Muslim.

Azumin kwana shida na watan sallah wato watan shawwal kenan Mustahabbine, wannan shine zancen mafiya yawa daga cikin malamai, wasu kuma sukace makaruhi ne saboda jin tsoron kada a dauka cewa shima wajibi ne kamar na Ramadan.

Yadda Ake Azumtansa

Malamai sunyi zantuka guda uku (3) kamar haka:

1. Yin Azumin guda shida ajare a farkon watan.

2. Yin Azumin ajere ko a rarrabe duka daya ne a kowani lokaci a cikin wata.

Fa'idan Azumin Shawwal

1. Yin Azumi Shida na Shawwal yana Cika ladan Azumin shekara.

2. Azumin Shawwal kamar Sallolin Nafiloli ne da'ake yi kafin da bayan Sallaolin farilla. Wanda suke cika nak'asa da tasamesu

2 Oct 2007

I'ITIKAFI

I'ITIKAFI

Dasunan Allah mai Rahama Mai Jinkai

Shine lazimtan masallaci da zama cikinsa da niyyan samun kusanci zuwa ga Allah. kuma malamai sunyi ittifak'I -wato sun hadu- akan cewa itikafi an shar'antashi kuma mustahabbi ne.

Tunatarwa: wasu mutane na kuskure ta yanda suke daukan cewa Itikafi, yakebanci manzan Allah ne Sallalahu Alaihi Wasallam shi kadai, wasu kuma suce hadisin Itikafi an shafe shi, wasu kuma suna dauka cewa Itikafi na dattawane ko akasin hakan, to duk wadannan kurakurai ne ba'a sha. Nana A'isha Allah yakara yarda agareta tace: (Lallai manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yakasance yanayin Itikafi a cikin goma na K'arshe na Ramadan har Allah yadauki ransa, sannan matansa sukayi Itikafi a bayansa) Bukhari. Ibn Hjar yace (Ba'a shafe hadisin ba kuma baya cikin abubuwan da suka kebanci ManzanAllah Sallallahu Alaihi Wasallam)fathul baari 4/272.

HUKUNCIN ITIKAFI

Mafi yawan malamai sun tafi akan cewa mustahabbi ne.

Imamu Malik Yace: (Nayi tunani akan al'amarin Itikafi, da abinda yazo akansa, da yanda musulmai suka barshi, tareda cewa manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam, be kasance yabarshi ba, se naga cewa sun barshi ne saboda yanada wahala akansu.)

Imam Azzuhri Yace: (akwai mamaki a Al'amarin musulmi! Sun bar Itikafi, tareda cewa Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam, be barshi ba tunda yazo Madinah , har Allah madaukakin Sarki yadauka ransa.)

SHARUDDAN ITIKAFI

1. MUSULUNCI: baya inganta ga wanda ba musulmi ba.

2. HANKALI: mahaukaci baya itikafi, saboda koda ibada ta wajibi bata zama dole akansu ba, andaga alkalami akansu.

3. NIYYA: sharad'I ce ga dukkan ibadodi, kuma duk aikmin da babu niyya a cikinsa ba karbabbe bane.

4. MASALLACI: ga namiji dolene yayi a masallaci, amma mace kuma anyi sabani akanta, Malam SUHNUNU Yace: (nace ma ibnul K'asim: menene zancen Imamu Malik gameda Itikafin mace tayi amasallacin jama'a? se yace Na'am, yace: a zancen Malik tayi Itikafi a masallacin gidanta? Se yace: Hakan baya burgeni, ana itikafi ne a masallacin da'aka yishi dan Allah.) Mudawwana 1/295.

Sheikh Aminul Hajj yace: (amma yafi rinjayen dalili awurina shine mace tayi Itikafinta a gidanta, wato wurin da takebance shi tana sallah a cikinsa.

5. AZUMI: wasu daga cikin malamai sukace kada mutum yayi itikafi face yaname Azumi, an tambayi Ibnul K'asim: (shin anayin itikafi batare da azumi ba a cikin zancen Malik? Se yace: ba'ayi se da Azumi. Wasu kuma sukace anayi koda mutum beyi Azumi ba, Sukace wannan shine ra'ayi mafi rinjayen dalili, saboda Hadisi Umar ingantacce da Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya Umarce shi da yayi itikafi yayin da yace masa yayi alwashin yin hakan a jahiliyya, kuma be ce masa yayi Azumi ba.

6. IZINI: dolene se miji yayi wa matarsa izini ko abinda ya mallaka na bawa ko baiwa, miji mace yana gida ne ko yayi tafiya dole tanemi izininsa, kuma idan yayi mata izini, to be kamata ya hanata ba kuma.

RUKUNNAN ITIKAFI

1. Zama a cikin Masallaci. 2. Nisantan Jima'I da abubuwan da zasu iya kaishi yin hakan. 3. Nisantar manyan laifuka. 4. Musulunci. 5. Hankali. 6. Tsarki daga Haila. Itikafi yana baci saboda rashin daya daga cikin wadannan.

ABUBUWAN DASUKE BATA ITIKAFI

1. FITA DAGA MASALLACI: baya halasta fita daga masallaci, In banda fita saboda: dan Biyan bukata kamar fitsari ko bayan gari, wankan janaba da na jumu'ah, cin abinci ko abin sha idan be iya ci ko sha a wurin da yake itikafi, idan yaji tsoron wuta ko sata kom rushewan gini, in aka fitar da shi da karfi, idan mace tayi haila da sharadin ta dawo da tayi tsarki, idan mijin mace yarasu ko yasake ta zata fita a mafi rinjayen zancen malamai biyu wasu sukace zata cigaba har seta kammala, fita saboda yin Umara, fita da mantuwa, idan yayi hauka ko suma.

2. YIN JIMA'I: saboda Allah yace: (kuma kada ku sadu dasu, alhalin kuna masu Itikafi a cikin masallatai…) Sur.Baqarah-186. haka sun bantan mace da sha'awa.

3. YIN RIDDA:wato fita daga musulunci

4. YIN MANYAN LAIFUKA: kamar yin zina da sata acikin itikafi, wanda mutane suna sakaci da daukan abin wani ko da kadan kuwa se a kiyaye.

5. YIN HAUKA KO SUMA: yana bata itikafi se dai idan yasami lafiya ko ya farfad'o to se yacigaba.

6. HAILA: idan mace tayi haila itikafinta ya baci, amma idan tayi tsarki se ta cigaba, na bayan be baciba.

ABUBUWAN DA BA'ASO GAME ITIKAFI

Ba'aso me itikafi ya shagaltu da abinda ba ambaton Allah ba, da kuma abinda ba dolene ba.

1. jayayya. 2. zagi damaganganun banza. 3. Yin giiba da Annamimanci. 4. Kallon abinda yake haramun. 5. Rashin yin magana gaba daya tun daga safe har dare da sunan bauta.

Tunatarwa: wasu daga cikin daliban ilimi se kaga suna zuwa itikafi da wasu littafai na karatunsu suna yin muraja'a, ba haramun bane amma kamata yayi tunda kwanakine yan kadan a cikin shekara, meze sa bazakayi hakuriba, sauran kwanakin shekara kayi acikinsu.

ABUBUWAN DASUKA HALASTA GAME ITIKAFI

1. Yin wanka da canza kaya, da sanya kayan da yakeso.

2. Cin Abinci da Shan Abin Sha a cikin masallaci.

3. Yin magan da yan uwa, amma ba'ason yawaita surutu da mutane.

4.Ya nemi Aure ko a daura masa Aure.

5. Yin Aski da yanke Farce.

6. Sanya turare.

ABUBUWAN DA SUKE MUSTAHABBI GA ME ITIKAFI

1. Mustahabbi ne ga me itikafi, yakafa tanti da ze kangeshi daga jama'a, inbe samu ba se ya lazimce wurin da babu jama'a ta yanda baze barshi ba seda larura.

2. kiyaye yin Sallah cikin jama'a, da nafiloli.

3. Yawan karatun alk'ur'ani, da rashin shagaltuwa da abinda ba ruwa.

4. Yawan ambaton Allah, zikiri, da tasbihi.

5. Yin azumi a cikin wantan da ba ramadan, ga wanda zeyi itikafi da rana.

6. Yawan yin kokari wajen d'a'a.

MAFI KARANCIN ITIKAFI DA MAFI YAWANSA

Itikafin neman lada baya da kad'an ko mafi yawa, se dai wanda yayi Itikafi a goman k'arshe na Azumin kada ya fita se idan anga watan Sallah wato Shawwal, malamai sun hadu akan cewa baya da mafi yawa, amma sunyi maganganu akan karancinsa, wasu sukace mafi karancinsa Sa'a, wasu sukace Yini daya da dare, wasu sukace kwana goma.

Imamul k'urtabi yace: ( mafi karancin itikafi a wajen Malik, da Abu Hanifa, dare da yini….)

YAUSHE AKE SHIGA ITIKAFI KUMA YAUSHE AKE FITA

A. Shiga wajen itikafi:akwai zancen malamai guda biyu:

1. Shiga bayan sallar Asubahin ranar Ashirin da d'aya na Ramadan, saboda hadisin Nana A'isha Allah yakara mata yarda tace: (Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam idan ze shiga itikafi yana yin sallar Asubahi, sannan se yashiga wurin itikafinsa) Bukhari. kuma wannan shine mafi rinjayen dalili. Kuma mazhabinAhmad da Laith da Ishak'.

2. Shiga kafin rana r daren Ashirin da d'aya ta fad'i, wannan shine mazhabin Malamai hud'u

B. Fita daga itikafi: Ana fita daga wurin itikafi bayan ganin watan sallah, wasu kuma sukace mustahabbine ya bari har yayi sallar idi sannan ya tafi.

SIRRIN DA YAKE CIKIN I'ITIKAFI

Bauta tana da sirruka da hikimomi masu yawa, saboda ayyuka gaba daya, makewayansu itace Zuciya, kamar yanda Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Yace (..Kusaurara! lallai acikin jiki akwai wata tsoka wanda idan ta gyaru, to dukkan sauran jiki ya gyaru, kuma idan ta bace, to dukkan Sauran jiki ya baci, ku saurara! Itace zuciya.) Bukhari da Muslim.

To in muka duba zamuga cewa mafi yawan abubuwan da suke bata zuciya, sune sha'awan cin abinci da abin sha da saduwa da Iyali da Zancen da ba na dole ba, da barcin da ba na dole ba, da abokai da basu da wata fa'ida da sauran abubuwa dasuke kawar da zuciya daga yin abinda yake biyayya ne ga Allah, se Allah ya Shar'anta wasu abubuwa na lada da zasukare zuciya daga rud'ani da shagaltuwa daga ambaton Allah, kamar Azumi wanda yake hana mutum cin abinci da abin Sha da Saduwa da Iyali da rana. To wannan hanuwan daga wadannan abubuwan jin dadi, shine yake karfafa alak'a tsakanin mutum da Ubangijinsa, da fuskantar dashi ga Lahira, kena Azumi garkuwa ce datake kare zuciya daga abubuwan sha'awa da suke kawar da mutum daga yin biyayya ga Allah, duk da hanine wanda yake matsakaici saboda an halasta wa mutum wadannan abubuwa a cikin dare.

To haka shima Itikafi yanada Sirri me girma, shine Kare mutum daga yawan cakud'a da jama'a, da yawan magana, saboda me Itikafi yana shagaltuwane da karatun Alk'ur'ani da Tsayuwa –wato yin sallah- da Zikiri da yawan yin Addu'a da makamantansu, haka kuma akwai kariya daga yawan barci, tunda yazo ibada ne ba barci ba, to wadannan abubuwa barinsu shike kara sa zuciya ta fuskanci Allah.

ABUBUWAN TUNATARWA

* Wasu daga cikin malamai sun tafi akan cewa ba'ayin Itikafi se a masallatai guda Uku kamar yadda yazo a cikin Hadisi, na hani akan yin Itikafi a masallatan da basuba, manzan Allah Sallalahu Alaihi Waasallam yace (Babu Itikafi face a masallatai guda uku) imamu Tahawi. -Wato masallacin Harami wato Ka'abah da masallacin Madinah da masallacin Aqsa wato Kudus-, Malamai suka fassara shi da cewa hani ne na yin alwashin yin Itikafi a wani masallaci da tafiya zuwa gareshi saboda hakan se a wadannan masallatan kadai ya halatta, ayi hakan saboda duk malaman mazhabobi Hud'u sun hadu akan cewa ya halatta ayi a kowani masallacin Juma'a.

* wasu sukan bar ayyukansu na wajibi saboda suyi Itikafi, to yin hakan kuskure ne saboda shi Itikafi sunna ce, saboda haka ba'a barin abinda yake wajibi saboda Sunnah.

Ya Allah Ka Karba mana dukkan Ayyukanmu a cikin Watan Ramadana kasa Muna cikin Bayinka Yantattu dag Wuta kuma kadatarmu da daren Lailatul K'adari. Amiin

20 Sept 2007

Yin Busahara da Azumin Ramadana

Yin Bushara da Azumin Ramadan
Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya kasance yana yima Sahabbansa Bushara da shifa watan Ramadankamar yadda Imamu Ahmad da Imamu Nasa'I suka kawo Hadisin da Abu Hurairah ya ruwaito daga Manzan Allah Sallalahu Alaihi Wasallam yace manzan Allah yakasance yanayiwa Sahabbansa Bushara "Hak'ik'a watan Ramadana mai albarka yazo maku, Allah ya wajabta maku Azumtansa, Ana bud'e kofofin Aljanna acikinsa kuma ana kulle kofofin Wuta , kuma ana D'aure Shaidanu acikinsa, akwai dare da tafi wata dubu acikinsa…………"
Watan Ramadan Yanada Wadansu Falala:
1. Watan da'aka Saukarda Alk'ur'ani 2. watan Taraawih da Tahajjud. 3. Watan Tuba da Kankare Zunubai. 4. watan Daure Shaid'anu. 5. watan da'ake kulle kofofin Wuta. 6. watan da'ake bud'e kofofin Aljanna. 7. watan kyauta da Ihsani. 8. watan da'ake y'antawa daga wuta. 9. watan Lailatul K'adr. 10. watajnAddu'a. 11. watan Jihadi. 12. watan da'ake nunka Lada acikinsa. 13. watan Hak'uri da Godiya.
Wata Me Tarihi
Watan Ramadan Watane me Tarihi acikin Musulunci wanda acikinsa aka Samu da yawa daga cikin Nasarorin yak'i da Kafirai. Gasu kamar haka: Shekar Ta Farko: acikin Ramadan aka aika Sariyya ta farko k'ark'ashin jagorancin Hamza bn Abdulmutallib, se Sariyyan Ubaidah binil Harith, domin sanya tsoro acikin zukatan Kafirai. Shekar Ta Biyu: acikin Sha bakwai ga Ramadan akayi Yak'in Badar Alkubra. Shekar Ta Uku: a cikin Ramadan manzan Allah Sallahu Alaihi Wasallam ya Shirya Runduna a madinah domin su hana mushrikai dasuke son daukan Fansan Yak'in Badr. Shekar Ta Biyar: Shiryawa Yak'in Khandaq, anyi yak'in ne acikin watan Shawwal wato watan Sallah kamar yanda Imamu bnil Qayyim yace Sun shirya mashi da wata d'aya wato suna hakk'a ganuwa. Shekar Ta Shida: Sariyyan Gaalib bin Abdullah wanda ta kunshi mutum da'ri da talatin wanda sukayi nasara akan bani Abdullahi bn tha'alabah. Shekar Ta Takwas: Bud'e Makkah acikin Ashirin ga Ramadan Allah ya daukaka Addininsa da manzansa da muminaikuma ya tseratar da Dakinsa me alfarma daga Hannun Mushrikan K'uraishawa, manzan Allah Sallalalhu Alaihi Wasallalm ya Shigeta tare dashi akwai Sojojin Musulunci dubu Goma. Shekar Ta Tara: Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam shi da Sahabbaqnsa suka dawo daga Ykin Tabuka. Shekar Ta Sha Uku: Yak'in Buwaib yakasance cikin ramadan a wuri da ake kira Buwaib kusa da kufa a yau acikin k'asar Iraq inda Farisawa karkashin jagorancin Mahran da musulmai Karkashin Jagorancin Almuthanna bin Harithah wanda yaki me matikar muni ya afku daga karshe Allah yaba musulmai nasara, an kashe da dama daga cikin musulmi, sukuma Farisawa tsakanin wanda aka kashe da wanda suka fad'a cikin ruwan Furat wajen gudu kimanin Dubu D'ari kuma aka samu Ganima me yawa, daganan ne aka karya Lagwan Farisawa. Sannan se Bud'e Garin Nuuba, a kudancin masarkarkashin Jagorancin Abdullahi bin Sa'ad bin Abi Sarah, wandA hakan ya bud'e kofa ga muslunci wajen Yad'uwa a garuruwa da yawa. Shekar Ta 53: Bud'e TsibirinRuuds, a karkashin Junadah bn Abi Umaiyah. Shekar Ta 67: Aka Gusar da daular Mukhtar Athak'afi wanda aka kashe a sha hud'u ga ramadan karkashin jagorancin Gwamnan Basra Mus'ab bini Zubair. Shekar Ta 91: Bud'e Andalus a hannun D'arik' bin Yazid bawan Musa dan Nusair sannan se Yak'in D'urif, musa bin Nusair ya aika wani mutum daga cikin K'abilar Bar-Bar ana kiransa D'uraif da mutane dari hudu da dawakai dari, inda suka tafi suka kai farmaki a gefen tekun Andalus kuma suka dawo da nasara. Shekar Ta 102: Musulmai suka bud'e Faransa bayan sun kafu a Andalus wato Spain kenan, se suka fara yakan Arewaci da yak'I abayan duwatsun pranis wanda suke tsakaninn Andalus da Faransa wanda da yawa daga cikin dakaru suka jagoranta. Acikin dan wannan gajeren lokaci baze yiwu mu iya ambatan duk yakin da'akayi cikin Ramadana ba ko bayanai sosai gameda hakan, kawai munso bayyana wasu daga cikine kawai dan nuna muhimmancin wannan wata da tarihinsa wajen musulmi.

26 Aug 2007

Falalar Ramadan

Falalar Azumin watan Ramaadan Hadisi tabbatacce yazo cikin bukhari da muslim daga Abu Hurairah Allah yakara masa yarda yace"Manzan Allah Sallalahu Alaihi Wasallam Yace (Dukkan aikin dfa dan Adam yayi to nasane Duk aikin lada yanada guda goma makamancinsa, har zuwa a ninka masa sau dari bakwai,se Allah madaukakin Sarki yace: banda Azumi domin shi nawane kuma nine zansaka akansa, shi me Azumi yakame daga Sha'awarsa da abinci da abin sha saboda ni, me Azumi yanada Farin ciki guda biyu: farin ciki a lokacin daze sha ruwa da farin ciki lokacin gamuwa da ubangijinsa, kuma tabbas warin bakin me Azumi shi yafi dadi a wurin Allah akan Kanshin turaren Almiski). Allah ya kebance Azumi a wannan riwaya daga cikin ayyukan daake rubanyawa daga goma har zuwa dari bakwai saboda Azumi baya da adadi wajen Rubanyawa Allah shi yasan Adadin daze rubanyashi, domin shi Azumi yana daga cikin hakuri, Allah madukakin Sarki yace: ("Lallai Allah yana cikawa masu Hakuri ladansu ne batare da Iyakancewa ba"Sur. Zumar-10) kuma yazo cikin hadisi manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ma'anar Fadansa (Azumi nawane) ya jingina Azumi zuwa gareshi ne saboda acikin azumi akwai hana rai abinda aka haliccieta da

11 Aug 2007

TAUHIDI (kadaita Allah)

Dasunan Allah Mai Rahama Mai Jinkai
TAUHIDI (kad'aita Allah)
Shine kadaita Allah a cikin Bauta shi kadai batare da hadashi da wani ba, kuma shine Addinin da aka aiko Annabawa dashi gaba dayaAllah yakara masu Aminci, kuma Allah baze karbi wani Addini ba inba shiba, kuma baya karban Ayyukan bayi se dashi, domin shine Asalin da ake gina Addini akanshi, kuma duk sanda aka rasashi to aikin bawa baze amfane shiba. KARKASUWAN TAUHIDI Tauhidi yakasu zuwa kashi uku (3):
1. Tauhidin Rububiyyah (Reno) Shine kudurce cewa Allah, shine wanda ya halicci, dukkan halittu, yake azurtasu, kuma wannan Nau’i na Tauhidi babu wanda yake musunshi, har mushrikan farko sun tabbatar dashi, kamar su Abu Jahal, fir’auma ne kawai wanda yatabayin musun babu ubangiji, sun kasance suna shedawa cewa Allah shine wanda yake halitta, yake gudanar dakomai dake cikin duniya, shike rayawa, yake kashewa, Allah madaukakin Sarki yace “Kuma idan kuka tambayesu wanene wanda yahalicci Sammai da Kassai, yake gudanar da Rana da Wata? Tabbas zasuce maka shine Allah…..( Sur.Ankabut: 61) Se ikirarin dasu kayi be shigar dasu musulunci ba, kuma baze tseratar dasu daga Azaba ba, kuma bata kare masu dukiyoyinsu da dukiyoyinsu ba, saboda basu tabbatar da Tauhidin Uluhiyyah, sun hada Allah da wani cikin bauta.
2. Tauhidin Uluuhiyyah (Bauta) Shine kadaita Allah acikin dukkan Ayyukan bauta da ake kusanci zuwa ga Allah dasu, kamar Addu’a da Tsoro,da Fata, da Dogaro, da Kwadayi, da Tsorata, da Neman temako, da neman biyan bukaya, da yin yanka da Alwashi da makamantansu. Kuma Allah yasaukarwa manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam (“Kace an umarceni ne da in bautawa Allah ina me kadaita masa Addini” Sur. Zumar 11.) wato bauta Saboda haka mutum baze juya wani daga cikin ibada bag a wani daya daga cikin mala’iku ko wani Annabi ko wani Waliyyi ko Shehi, domin hakki ne na Allah, wanda kon yaba wanda bashi ba to yayi Shirka.
3. Tauhidin Asmaa’u was Siffat Shine imani da cewa Allah yana da zati wanda baya kama da sauran zatuttuka, yana da siffofin da b asa kamada sauran siffofi, kuma sunayensa suna nuni ne nuni na yanke shakka akan abinda abinda yake dashi na siffofin cika wayo kamala kai tsaye. Allah Subhanahu Wata’ala yace (“Babu wani abu da yayi kama dashi kuma shi me jine me gani “ Sur. Shuurah 11.) kuma da tabbatar da abinda Allah ya tabbatar ma kansa acikin littafinsa (Al’qur’ani)ko manzansa yatabbatar masa dashi tabbatarwa wacce take dacewa da girma da daukakarsa ba tare da kamantashi da wani abu ba, ko kwatantashi da wani ba, ko kore masa sifar, ko lankwasa ma’anarsa, ko yanda yake, baza muyi kokarin kamanta wani sashi na cikin siffofinsa ba da zukatanmu ko da tunaninmu, A’ah zmu bar abin kamar yanda yabamu labari. TO YAYA ZAMU SAMU TAUHIDI?
Zamu iya zama masu tauhidi ne, ta hanyar sanin Allah, wanene shi? da sanin hakikaninsa, a ilmance da kuma aiki da hakan, kuma shine Rai tajawu ko zuciya zuwa gareshi da soyaiya, da tsoro, da komawa zuwa gareshi, da dogaro akanshi, da Addu’a, da tsarkakeshi, da girmamashi da kuma yimasa bauta. Atakaice dai kada yazamana a zuciyar dan Adam daba na Allah ba, kuma bawa yazama baya nufin Allah da Shirka ko Bid’ah ko Sabo karaminsa da babbansa,kuma kada ya nuina kiyaiya ga duk abinda Allah yayi Umarni dashi to wannan tauhidi da kansa wato Laa ilaa ha illal Lah. MENENE MA’ANAR LAA’ILAA’HA ILLAL LAHU?
Ma’ana shine babu abin da’ake bautawa da cancanta a Sama da Kasa face Allah shi kadai baya da abokin taraiya, domin abubuwan da’ake bauta mawa baatattu suna da yawa, se dai abinda ya can-can ci bautan shine Allah shi kadai.Allah Subhanahu Wata’ala yace: (“ Saboda haka Allah shine Ubangiji na gaskiya, kuma tabbas an\binda suke kira wanda bashi baataccene, kuma lallai Allah shine madaukaki kuma me girma” Sur.alhajj:62) ba ma’anarta ba Babu mahalicci se Allah kamar yadda wadansu jahilai suke tsammani, domin kafiran Kuraishawa wanda Allah ya’aikoda manzo a cikinsu sun kasance suna sheda cewa Allah shine mahalicci me gudanar da al’amuran duniya shi kadai baya da abokin taraiya kamar yanda Allah yace: (“Shin yanzu za’a sanya Abin bauta yazama ubangiji guda daya Lallai wannan abune me ban mamaki” Sur. Saad:5) sun fahimci cewa wannan kalma lallai tana bata bautawa duk wanda ba Allah ba, kuma tana takaita bauta ga Allah shi kadai sukuma basa son haka, saboda hakane manzan Allah ya yakesu har se sun Shaida da Laa ilaa ha illal laahu kum subata hakkinta, shine kadaita Allah da bauta shi kadai. Wanna ke bata ikirarin da wadansu keyi cewa ma’anar Laa ila ha illal laahu shine kace Allah yana nan kuma shine wanda yayi halitta, yake gudanar da al’amura kuma wanda yayi hakan yana da Tauhidi koda yayi ma wani bauta kamar Rokon wadanda suka mutu suke cikin kabari,d yimusu alwashi, da neman kusancinAllah tahanyarsu, da neman Albarka (tabarruki) da yin dawafi a kabarbura da neman albarka da kasar kabarin kamar yanda muke ganin a kabarin Shehu dan fodio dake sokoto. Hakika kafiran Kuraishawa sun san cewa Laa ilaa ha illal lahu tana bukatan aiki shine barin bautawa wanda ba Allah ba, kuma idan suka fadeta suka cigaba da bauta ma gumaka to zasu war-ware musuluncinsu sukuma bas son haka sukeba, abin mamaki yau zaka musulmi suna bauta ma Allah kuma suna neman temakon wanda ba Allah, suna kiran sunayen wasu matattu na mutanen kwarai, suna war-ware musuluncinsu. Tur da wanda Abu jahal, da Abu lahab suka fisu sanin ma’anar laa ilaa ha illal lahu. RUKUNNAN KALMAR TAUHIDI
Kalmar tauhidi tana da rukunnai guda biyu (2). korewa: tana kore bautan kowani irin abin bauta. Tabbatarwa: tana tabbatar da bauta ga Allah madaukakin Sarki shi kadai batareda hadashi da wani ba. MENENE KE WAR-WARE KALMAR TAUHIDI?
Abubuwan dasuke war-ware (bata) Kalmar tauhidi suna da yawa, amma ga wadansu daga ciki:
Na Farko: Shirka da Allah a cikin bauta, Allah madaukakin Sarki yace: (“Lallai Allah baya gafartama wanda yahada shi dawani, amma yana gafarta ma abinda ba haka ba (shirka) ga wanda yaso” Sur.Nisaa’i:116) kuma yace: (“lalai ne duk wanda yayi Shirka da Allah, to hakika Allah ya haramta masa Aljanna, kuma makomansa itace wuta, kuma Azzalumai basu da wani me temako” Sur.ma’idah:72) kuma yana daga cikin shirka, kiran wani da ba Allah ba, Idan wata musiba (fitina) tazo, yi ma Aljanu yanka ko kabari.
Na Biyu: Duk wanda yasanya wani tsakaninsa da Allah, yana Rokonsu, yana kiransu, yana neman cetonsu, yana dogaro a kansu, ya kafirta da ijmaa’in malaman musulunci.
Na Uku: Duk wanda be kafirta mushrikai ba ko yayi shakkan kafircinsu, ko yake gyara abinda suke akai kaman yan gurguzu. To ya kafirta.
Na Hudu: Duk wanda yake kudurin cewa shiryawan da ba ta Annabi ba, shi yafi cika da dai-dai akan shiryarwar manzan Allah Sallal lahu alaihi wasallam, ko hukuncin wani yafi hukuncinsa, kamar wanda yake fifita tsarin turawa akan Shri’ar musulunci to ya kafirta.
Na Biyar: Duk wanda ya kyamaci wani daga cikin abinda manzan Allah yazo dashi to koda yayi aiki dashi ya kafirta Allah madaukakin Sarki yace (“Hakan saboda kafirai sun kyamaci abinda Allah ya saukar se yabata ayyukansu”Sur.muhammad:9) Na Shida: Duk wanda yayi izgili da wani abu dake cikin Addinin da manzon Allah yazo dashi, ladan dake ciki, ko azaban dake ciki ya kafirta Allah madaukakin Sarki yace (“kace masu shin yanzu da Allah, da Ayoyinsa, da manzansa kuke yiwa izgili? Kada kukawo uzuri hakika kunzama kafirai bayan kuna masu imani...Sur.tauba:65-66)
Na bakwai: Sihiri duk wanda ya aikatashi ko ya yardaq dashi,ya kafirta Allah madaukakin Sarki yace: (“ kuma basa karantar da kowa sihiri – aljanu – face .........................................................................................
Na takwas: duk wanda.............. zamu cigaba isha Allah