MARABA DA ZUWA SHAFINMU NA MUSULUNCI

20 Jul 2008

SIFFAR BARCIN MANZAN ALLAH SALLALLAHU WASALLALAM

SIFFAR BARCIN MANZAN ALLAH SALLALLAHU WASALLALAM

  • Ya kasance yana Barci a Farkon dare, ya raya karshensa – wato yanayin Sallah a cikinsa kenan- Bukhari da Muslim.

Ø Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam Ya Kasance idan ya hau kan shinfidarsa zeyi Barci yana cewa : “ Bismikallahumma Amutu Wa’ahyaa” (Ma’ana Da sunanka Ubangiji, nake Mutuwa kuma nake Rayuwa. Mutuwa = Yin barci , Rayuwa = Farkawa daga barci) kuma idan ya farka daga barci yana cewa “ Alhamdu lil lahil ladhi Ahyaana ba’ada ma Amaatana Wa ilaihin nushur” ( Ma’ana Dukkan godiya ta tabbata ga Allah Wanda ya Rayamu bayan ya kashe mu, kuma gareshi tashi yake) Muslim.

Ø Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Ya Kasance idan ze kwanta barci yana sanya tafin Hannunsa na dama kar-kashin kuncinsa na dama se Yace: “Rabbi Qini azabaka Yauma tab’athu ibadika” (Ma’ana Ya ubangiji ka tsareni daga Azabarka ranar da zaka tashi bayinka –wato ranar Lahira kenan) Tirmidhi .

Ø Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam Ya Kasance a kowani dare idan ze kwanta yana hada tafukan Hannayensa se ya huresu Ya karanta (Kulhuwallahu Ahad) da (Kul’a’uzu birabbil Falaq) da (Kul’a’uzu bi rabbin Nas), sannan ya shafama inda ya sauwaka a jikinsa, yana farawa da kansa se fuskarsa da barin gaba na jikinsa, yana yin hakan sau uku. Bukhari da Muslim.

Ø Ya Kasance yana barci a kan matashin kai (pillow) na Fata cikinsa an cikashi da gashin bishiyar dabino Ahmad.

Ø Shimfidar da Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Ya Kasance yana barci akanta ta Fata ce da aka cika da gashin bishiyar dabino Muslim.

Ø Nana Aisha Allah ya kara Yarda agareta tace Ya Manzan Allah Shin kana barci ne kafin kayi Sallar Witri? Se Yace: “ Yake Aisha: Idanuwana suna Barci amma Zuciya ta bata Barci” Bukhari da Muslim.