MARABA DA ZUWA SHAFINMU NA MUSULUNCI

26 Aug 2007

Falalar Ramadan

Falalar Azumin watan Ramaadan Hadisi tabbatacce yazo cikin bukhari da muslim daga Abu Hurairah Allah yakara masa yarda yace"Manzan Allah Sallalahu Alaihi Wasallam Yace (Dukkan aikin dfa dan Adam yayi to nasane Duk aikin lada yanada guda goma makamancinsa, har zuwa a ninka masa sau dari bakwai,se Allah madaukakin Sarki yace: banda Azumi domin shi nawane kuma nine zansaka akansa, shi me Azumi yakame daga Sha'awarsa da abinci da abin sha saboda ni, me Azumi yanada Farin ciki guda biyu: farin ciki a lokacin daze sha ruwa da farin ciki lokacin gamuwa da ubangijinsa, kuma tabbas warin bakin me Azumi shi yafi dadi a wurin Allah akan Kanshin turaren Almiski). Allah ya kebance Azumi a wannan riwaya daga cikin ayyukan daake rubanyawa daga goma har zuwa dari bakwai saboda Azumi baya da adadi wajen Rubanyawa Allah shi yasan Adadin daze rubanyashi, domin shi Azumi yana daga cikin hakuri, Allah madukakin Sarki yace: ("Lallai Allah yana cikawa masu Hakuri ladansu ne batare da Iyakancewa ba"Sur. Zumar-10) kuma yazo cikin hadisi manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ma'anar Fadansa (Azumi nawane) ya jingina Azumi zuwa gareshi ne saboda acikin azumi akwai hana rai abinda aka haliccieta da

11 Aug 2007

TAUHIDI (kadaita Allah)

Dasunan Allah Mai Rahama Mai Jinkai
TAUHIDI (kad'aita Allah)
Shine kadaita Allah a cikin Bauta shi kadai batare da hadashi da wani ba, kuma shine Addinin da aka aiko Annabawa dashi gaba dayaAllah yakara masu Aminci, kuma Allah baze karbi wani Addini ba inba shiba, kuma baya karban Ayyukan bayi se dashi, domin shine Asalin da ake gina Addini akanshi, kuma duk sanda aka rasashi to aikin bawa baze amfane shiba. KARKASUWAN TAUHIDI Tauhidi yakasu zuwa kashi uku (3):
1. Tauhidin Rububiyyah (Reno) Shine kudurce cewa Allah, shine wanda ya halicci, dukkan halittu, yake azurtasu, kuma wannan Nau’i na Tauhidi babu wanda yake musunshi, har mushrikan farko sun tabbatar dashi, kamar su Abu Jahal, fir’auma ne kawai wanda yatabayin musun babu ubangiji, sun kasance suna shedawa cewa Allah shine wanda yake halitta, yake gudanar dakomai dake cikin duniya, shike rayawa, yake kashewa, Allah madaukakin Sarki yace “Kuma idan kuka tambayesu wanene wanda yahalicci Sammai da Kassai, yake gudanar da Rana da Wata? Tabbas zasuce maka shine Allah…..( Sur.Ankabut: 61) Se ikirarin dasu kayi be shigar dasu musulunci ba, kuma baze tseratar dasu daga Azaba ba, kuma bata kare masu dukiyoyinsu da dukiyoyinsu ba, saboda basu tabbatar da Tauhidin Uluhiyyah, sun hada Allah da wani cikin bauta.
2. Tauhidin Uluuhiyyah (Bauta) Shine kadaita Allah acikin dukkan Ayyukan bauta da ake kusanci zuwa ga Allah dasu, kamar Addu’a da Tsoro,da Fata, da Dogaro, da Kwadayi, da Tsorata, da Neman temako, da neman biyan bukaya, da yin yanka da Alwashi da makamantansu. Kuma Allah yasaukarwa manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam (“Kace an umarceni ne da in bautawa Allah ina me kadaita masa Addini” Sur. Zumar 11.) wato bauta Saboda haka mutum baze juya wani daga cikin ibada bag a wani daya daga cikin mala’iku ko wani Annabi ko wani Waliyyi ko Shehi, domin hakki ne na Allah, wanda kon yaba wanda bashi ba to yayi Shirka.
3. Tauhidin Asmaa’u was Siffat Shine imani da cewa Allah yana da zati wanda baya kama da sauran zatuttuka, yana da siffofin da b asa kamada sauran siffofi, kuma sunayensa suna nuni ne nuni na yanke shakka akan abinda abinda yake dashi na siffofin cika wayo kamala kai tsaye. Allah Subhanahu Wata’ala yace (“Babu wani abu da yayi kama dashi kuma shi me jine me gani “ Sur. Shuurah 11.) kuma da tabbatar da abinda Allah ya tabbatar ma kansa acikin littafinsa (Al’qur’ani)ko manzansa yatabbatar masa dashi tabbatarwa wacce take dacewa da girma da daukakarsa ba tare da kamantashi da wani abu ba, ko kwatantashi da wani ba, ko kore masa sifar, ko lankwasa ma’anarsa, ko yanda yake, baza muyi kokarin kamanta wani sashi na cikin siffofinsa ba da zukatanmu ko da tunaninmu, A’ah zmu bar abin kamar yanda yabamu labari. TO YAYA ZAMU SAMU TAUHIDI?
Zamu iya zama masu tauhidi ne, ta hanyar sanin Allah, wanene shi? da sanin hakikaninsa, a ilmance da kuma aiki da hakan, kuma shine Rai tajawu ko zuciya zuwa gareshi da soyaiya, da tsoro, da komawa zuwa gareshi, da dogaro akanshi, da Addu’a, da tsarkakeshi, da girmamashi da kuma yimasa bauta. Atakaice dai kada yazamana a zuciyar dan Adam daba na Allah ba, kuma bawa yazama baya nufin Allah da Shirka ko Bid’ah ko Sabo karaminsa da babbansa,kuma kada ya nuina kiyaiya ga duk abinda Allah yayi Umarni dashi to wannan tauhidi da kansa wato Laa ilaa ha illal Lah. MENENE MA’ANAR LAA’ILAA’HA ILLAL LAHU?
Ma’ana shine babu abin da’ake bautawa da cancanta a Sama da Kasa face Allah shi kadai baya da abokin taraiya, domin abubuwan da’ake bauta mawa baatattu suna da yawa, se dai abinda ya can-can ci bautan shine Allah shi kadai.Allah Subhanahu Wata’ala yace: (“ Saboda haka Allah shine Ubangiji na gaskiya, kuma tabbas an\binda suke kira wanda bashi baataccene, kuma lallai Allah shine madaukaki kuma me girma” Sur.alhajj:62) ba ma’anarta ba Babu mahalicci se Allah kamar yadda wadansu jahilai suke tsammani, domin kafiran Kuraishawa wanda Allah ya’aikoda manzo a cikinsu sun kasance suna sheda cewa Allah shine mahalicci me gudanar da al’amuran duniya shi kadai baya da abokin taraiya kamar yanda Allah yace: (“Shin yanzu za’a sanya Abin bauta yazama ubangiji guda daya Lallai wannan abune me ban mamaki” Sur. Saad:5) sun fahimci cewa wannan kalma lallai tana bata bautawa duk wanda ba Allah ba, kuma tana takaita bauta ga Allah shi kadai sukuma basa son haka, saboda hakane manzan Allah ya yakesu har se sun Shaida da Laa ilaa ha illal laahu kum subata hakkinta, shine kadaita Allah da bauta shi kadai. Wanna ke bata ikirarin da wadansu keyi cewa ma’anar Laa ila ha illal laahu shine kace Allah yana nan kuma shine wanda yayi halitta, yake gudanar da al’amura kuma wanda yayi hakan yana da Tauhidi koda yayi ma wani bauta kamar Rokon wadanda suka mutu suke cikin kabari,d yimusu alwashi, da neman kusancinAllah tahanyarsu, da neman Albarka (tabarruki) da yin dawafi a kabarbura da neman albarka da kasar kabarin kamar yanda muke ganin a kabarin Shehu dan fodio dake sokoto. Hakika kafiran Kuraishawa sun san cewa Laa ilaa ha illal lahu tana bukatan aiki shine barin bautawa wanda ba Allah ba, kuma idan suka fadeta suka cigaba da bauta ma gumaka to zasu war-ware musuluncinsu sukuma bas son haka sukeba, abin mamaki yau zaka musulmi suna bauta ma Allah kuma suna neman temakon wanda ba Allah, suna kiran sunayen wasu matattu na mutanen kwarai, suna war-ware musuluncinsu. Tur da wanda Abu jahal, da Abu lahab suka fisu sanin ma’anar laa ilaa ha illal lahu. RUKUNNAN KALMAR TAUHIDI
Kalmar tauhidi tana da rukunnai guda biyu (2). korewa: tana kore bautan kowani irin abin bauta. Tabbatarwa: tana tabbatar da bauta ga Allah madaukakin Sarki shi kadai batareda hadashi da wani ba. MENENE KE WAR-WARE KALMAR TAUHIDI?
Abubuwan dasuke war-ware (bata) Kalmar tauhidi suna da yawa, amma ga wadansu daga ciki:
Na Farko: Shirka da Allah a cikin bauta, Allah madaukakin Sarki yace: (“Lallai Allah baya gafartama wanda yahada shi dawani, amma yana gafarta ma abinda ba haka ba (shirka) ga wanda yaso” Sur.Nisaa’i:116) kuma yace: (“lalai ne duk wanda yayi Shirka da Allah, to hakika Allah ya haramta masa Aljanna, kuma makomansa itace wuta, kuma Azzalumai basu da wani me temako” Sur.ma’idah:72) kuma yana daga cikin shirka, kiran wani da ba Allah ba, Idan wata musiba (fitina) tazo, yi ma Aljanu yanka ko kabari.
Na Biyu: Duk wanda yasanya wani tsakaninsa da Allah, yana Rokonsu, yana kiransu, yana neman cetonsu, yana dogaro a kansu, ya kafirta da ijmaa’in malaman musulunci.
Na Uku: Duk wanda be kafirta mushrikai ba ko yayi shakkan kafircinsu, ko yake gyara abinda suke akai kaman yan gurguzu. To ya kafirta.
Na Hudu: Duk wanda yake kudurin cewa shiryawan da ba ta Annabi ba, shi yafi cika da dai-dai akan shiryarwar manzan Allah Sallal lahu alaihi wasallam, ko hukuncin wani yafi hukuncinsa, kamar wanda yake fifita tsarin turawa akan Shri’ar musulunci to ya kafirta.
Na Biyar: Duk wanda ya kyamaci wani daga cikin abinda manzan Allah yazo dashi to koda yayi aiki dashi ya kafirta Allah madaukakin Sarki yace (“Hakan saboda kafirai sun kyamaci abinda Allah ya saukar se yabata ayyukansu”Sur.muhammad:9) Na Shida: Duk wanda yayi izgili da wani abu dake cikin Addinin da manzon Allah yazo dashi, ladan dake ciki, ko azaban dake ciki ya kafirta Allah madaukakin Sarki yace (“kace masu shin yanzu da Allah, da Ayoyinsa, da manzansa kuke yiwa izgili? Kada kukawo uzuri hakika kunzama kafirai bayan kuna masu imani...Sur.tauba:65-66)
Na bakwai: Sihiri duk wanda ya aikatashi ko ya yardaq dashi,ya kafirta Allah madaukakin Sarki yace: (“ kuma basa karantar da kowa sihiri – aljanu – face .........................................................................................
Na takwas: duk wanda.............. zamu cigaba isha Allah

6 Aug 2007

Shi yasa aka fifitasu....

Dasunan Allah mai Rahama mai Jinkai WADANSU ABUBUWA DA'AKA KEBANCE AL'UMMAR MUSULMI DASU AKAN SAURAN AL'UMMU Hakika Allah madaukakin Sarki ya karrama A'ummar musulunci, kuma ya daukakata akan sauran al'ummu, ya kebanceta da wasu abubuwa, ita kadai. Tabbas tasami wannan girmane, saboda daraja da falalan Annabinta Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallam, da imani datayi dashi. Daga cikin daukakashi da Allah yayi bayan yazabeshi daga cikin halittu,ya zaba masa Abokai (wato sahabbai) matemaka agareshi. Allah madaukakain Sarki yace ( "shine wanda yazabeku –sahabbai- kuma be sanya maku wani abu me wahala acikin Addini ba" ) (Sur. Hajji -78.) kuma yace ( "kuma haka muka sanyaku Al'umma mafificiya domin kuzamo masu sheda ga mutane (Annabawan dasuka gabata akan mutanensu) kuma manzo yazama me shesa akanku….") Sur. Baqarah-143). Saboda haka ne yazama dole akan muslmai dasusan abinda suke ciki na ni'ima,da kuma abinda suke akai na alkhairi, don suyi rikoda shi kumasuyi rikodashi kuma suyi aiki domin yadashi……………………….zamu cigaba insha Allah

4 Aug 2007

MATSAYIN SALLAH

Dasunan Allah Mai Rahama Mai Jinkaiِ
SALLAH
Ita Dayace daga cikin rukunnan musulunci guda biyar, wanda Allah maduakakin sarki ya wajabtata guda Hamsin(50) yayin da manzan Allah Sallallaahu Alaihi Wasallama yaje Mi'iraaji (wato Sama) yakarbo ta yayi ta neman ubangiji da ya ragemana ita har aka rageta zuwa guda biyar (5) kamar yadda take a yau saboda tausayin manzan Allah garemu Sallalahu Alaihi Wasallam. Kuma manzan Allahn Sallalahun Alaihi Wasallam yace "Itace farkon abinda za'ayi Wa bawa sakamako (hisabi) Ranar k'iyama Idan tayi kyau dukkan Sauran aiki zasuyi kyau bawa yasama tsira kuma idan tayi muni to dukkan sauran ayyuka bazasu amfane bawaba. Sannan kafin Sallar da bawa yakeyi tasami karbuwa se idan tadace da yadda manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallama yayita kuma ya karantar domin fadan Ma'aiki "Kuyi Sallah Kamar yadda kuka ina yin Sallah", Sannan an wajabta yinta acikin jama'a (wato Jam'i a masallaci). Kuma wanda duk yabarta to yabar musulunci kamar yadda ma'aiki Tsira da Amincin Allah su kara Tabbata Agareshi yace " Alkawarin dake tsakaninmu dasu shine Sallah duk wanda yabarta to ya kafirta". To idankowannan shine al'amarin Sallah to yazama dole akan kowane muslmi dayasan mecece Sallah? Kuma menene Hukunce-Hukuncenta? da abubuwan dasu batata domin ta kasancce karbabaiya a wajen Allah Madaukakin Sarki…………….

MABUDI

Dukkan yabo da Godiya sun tabbata ga Allaah madaukakin sarki Tsira da Amincin Allaah su kara tabbata ga manzan Allaah da Iyalan gidansa da duk wadanda suka bi karantarwarsa wato sunnarsa har zuwa ranar sakamako. Amin