MARABA DA ZUWA SHAFINMU NA MUSULUNCI

1 May 2008

NA UKU (3)

NA BIYAR: AMBATON ALLAH (WATO YIN ZIKIRI)

Ambaton Allah yana daga mafi girman dalili na samun Tabbatuwa.

Kayi tunani akan kusanci da juna da umarni guda biyu sukayi cikin Fadinsa madaukakin Sarki : [ Yaku Wadanda sukayi Imani Idan kun hadu da wata Jama’a – wato kafirai kenan a Yaki – To ku tabbatu, kuma ku ambaci Allah da yawa…] [Sur. Al-anfal- 45]. Ya sanya Zikiri a matsayin mafi girman abinda yake temakawa wajen tabbatuwa a fagen Jihadi.

“ Kuma kayi tunanin Rumawa da Farisawa a Yakukan da’akayi da kuma Masu Zikiri duk da Karancinsu.

Sannan da Menene Annabi Yusuf (Alaihis Salam) Ya samu Tabbatuwa sanda Fitinar Matannan me mulki da tsananin Kyawo ta nemeshi akanta? Shin be shiga cikin Ganuwan (Ma’azal lah) ba Ma’ana Ina neman kariya daga Allah kuma shin rundunar Sha’awa bata bal-balce ba akan katangan da suke kareshi?.

To hakane Yin Zikiri yake aiki wajen Tabbatar da Muminai.

HANYOYIN TABBATUWA NA UKU (3)

NA SHIDA: MUSULMI YAYI KWAɗAYIN BIN INGANTACCEN TAFARKI

Ingantaccen tafarki ƙwãya ɗaya tal, daya zama tilas kowani musulmi yabi, shine: tafarkin Ahlus-sunnah wal-jama’a. tafarkin Jama’a da’aka temaka, kuma Jama’a ne tseratattu, mãsu tsabtatattan Aƙida, da manhaji ingantacce, da bin Sunna da dalili, da banbanta daga maƙiyan Allah, da rabuwa da masu ɓata.

Idan kuma har kanã so kasan matsayin bin ingantaccen tafarki, a wajen tabbatuwa, to kayi tunani, kuma ka tambayi kanka: Me yasa dayawa daga cikin wadanda suka gabãta da wadanda suka biyo bãyansu suka halaka, kuma suka ruɗe, duga-dugansu suka kãsa tabbata akan tafarki madai-daici? kuma basu mutu akansa ba? Ko kuma A’A sun isa zuwa gareshi bayan sun ƙãrar da mafi yawan rayuwarsu, kuma sun ɓatar da mafi tsãdan lokutansu a cikin rayuwansu?.

Zakaga ɗayansu yana ta yãwo, a cikin masaukai na bidi’a da ɓata, daga Falsafa zuwa ga ilimin kalami wato zance, daga Mu’utazilanci zuwa ga Tahrifi da tãwili zuwa tafwidi zuwa ga Murji’anci, daga wata darik’a cikin Sũfanci zuwa wata.

To haka Y’an bidi’a, sũma sunã da rũɗu, da rashin natsuwa, ka duba kaga yanda aka hanãma Y’an Zance (wato Ahlul kalam) tabbatuwa a lokacin mutuwa, magabata Sukace: “Wanda sukafi kõwa Shakka a lokacin mutuwa sune Y’an Zance (Ahlul kalam)”.

Sedai kayi tunani kaga, shin akwai koda mutum ɗaya daga cikin Ahlus Sunna wal-jama’a, da yataɓa barin tafarkinsa, ya ƙyamaceshi, yayi fushi dashi, bayan yã bishi, yã sanshi, yã fahimceshi? Zata yiwuwa, Mutum ya barsa Saboda son rai, ko dan kwaɗayin abin duniya, ko saboda Shubuha da’aka bijiroma hankalinsa me rauni da’ita, Amma baya barinsa, saboda wai yaga wani tafarkin da yafishi inganci, ko yagãno cewa shi ɗin ɓatane.

Kuma abinda ze gaskata hakan shine: Lokacin da Hiraƙal ya tambayi Abũ Sufyan, gameda mãsu bin Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallamr, Se Hiraƙal Yace ma Abũ Sufyan: “Shin a cikinsu akwai koda Mutum ɗaya da yataɓa yin RIDDA -wato ya fita daga Addinin-, ya yi fushi dashi ya ƙyamace shi, bayan ya shiga cikinsa?” Se Abũ Sufyan Yace: A’a se Hiraƙal Yace: To hakanan Imãni yake, idan ya cakuɗa –wato ya haɗu- da Zũciya”.

Sau dayawa Munji cewa Shugabanni sun bar Masuaki na Bidi’a, wasu kuma Allah ya shiryasu, sun b’ar ɓata sun koma zuwa ga Mazhabin Ahlus Sunna Wal-jama’a, suna masu nuna ƙyama da fushi ga tafarkin da suke a kansa na farko,

Shin ko mun taɓa jin Akasin hakan?!

To idan har kanã son tabbatuwa, to wãjibi ne kabi tafarkin Muminai.

NA BAKWAI: TARBIYYA:

Tarbiyya ta Imãni da ilimi da fahimta, wanda take akan mataki - mataki, Ma’auni ne daga cikin ma’aunan Tabbatuwa.

TARBIYYAN IMANI: Itace take kãre zukãta da rãyuka. kuma Ana samun ta ne ta hanyar Jin tsoron Allah, da fãta, da Soyayya, wandu suke kõre bũshewar zuciya, sakamakon yin Nisa da Nassosin Alƙur’ani da Hadisan Manzan Allah Sallallahu Alihi Wasallamr, da durƙusãwa ga Zantuttukan Mazaje.

TARBIYYA TA ILIMI: Itace wacce take tsaye akan dalili ingantacce, wanda take kõre yin taƙalidanci da ….makoma…. abin zargi.

TARBIYYA TA FAHIMTA: Itace wacce da ita zãka san tafarkin mãsu laifi (mujurimai), da karanta Shirye-Shiryen maƙiya Musulunci, kasan abubuwan da suke fãruwa a gefenka, ka fahimci abubuwan dasuke fãruwa, dan ka iya yin hukunci akansu, Hakan ze kõre maka dõɗewa da zama a wuri ɗaya da rashin fita daga cikin bi’a da take Y’ar karama Iyakantacciya.

TARBIYYAN MATAKI-MATAKI: Itace Wacce zatabi da Musulmi da kaɗan da kaɗan (da sannu da sannu), har ta ɗagãshi zuwa ga matakin da ze cika, da tsari dai-daitacce, wanda hakan ze kõre masa Yin gaggawa da sauri da tsallake, wanda yake ruguzawa.

Kuma domin mu san mahimmancin wannan gaɓan cikin sassan tabbatuwa, to se mukoma zuwa ga Tarihin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasllamr, kuma muyiwa kawunanmu tambaya?

**Menene asalin abinda ya tabbatar da Sahabban Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam, a lokacin da’ake gãna masu Azãba?

** Me yasa Bilãl da Khabbab da Mus’ab da Ãlu Yãsir da sauransu, daga cikin masu rauni, kai har Manyan Sahabbai sũma a killacewan da’akayi musu a Bani Shi’ab da sauransu?.

** Shin zeyiwu tabbatuwansu ta kasance ba tãre da wata Tarbiyyaba me zurfi ba daga Fitilan Annabta, wanda ta tarbiyyantar da rãyukansu?

Mu ɗauka wannan Sahabin ƙhabbãb binil Art t Allah yakãra Yarda a gareshi, wanda Shugabansa ta kasance tana ƙõna wayã, irin wanda ake gasa nãma dashi, har se tayi Jãjur, sannan se ta ɗõra bayansa akai –wato tana gasa bayansa kaman nãma kenan a bũɗe –, Kuma Mai dake fitõwa daga bayansa ne, idan ya kwararo, yake kasheta. To Me yasa yayi haƙuri akan haka?

Bilãl Kuma yana cãn ƙarƙashin dũtse a kan Sahãra, SUMAIYA kuma tana ɗaure cikin Mari. Gawata tambaya da’aka samu a Lokacin dasuke Madina: Su wãnene suka tabbata tãre da Manzan Allah Sallallanu Alaihi Wasallam r a Yaƙin Hunãin lõkacin da aka sãmu Nasara akan dayawa daga cikin Musulmai? Shin Sãbabbun Musulunta ne, ko wanda suka musulunta a Yãƙin Makka, wanda basu sami isasshen lõkaci na tarbiyya ba a Makarantar Annabta, wanda dayawa daga cikinsu sun fita ne saboda neman Ganima? A’a...Mafi yawa cikin waɗanda suka tabbata sune: waɗannan zãɓaɓɓun Muminan, da suka sãmu adadi me girma na Tarbiyya daga wajen Manzan Allah Sallallanu Alaihi Wasallam r . Ba domin akwai Tarbiyya ba, Shin kãna ganin waɗannan Sahabban zãsu tabbata?

TAMBAYA : Hadisin dayake cewa “ Kada kuyi Azumi ranar Asabar Face abinda aka Farlanta maku – wato Ramadan –“ shin Hadisin Ingantacce ne, kuma menene ma’anar Hadisin kuma shin ya kunshi dukkan Azumi ne?

ME BADA AMSA: Shaikh Abdur rahman bin Jibrin Mamba a cikin Majalisar manyan malamai masu fatawa a kasar Saudi Arabia.

AMSA: an kebance ranar Asabar ne da Hani saboda yahudawa sun kasance suna barin aiki a cikinta, se aka hana girmama ranar saboda kada ayi kamance – ceniya dasu, kuma ya halarta a Azumce Asabar idan akwai sababi, Kaman wanda yake Azumi rana ya sha ruwa rana, haka idan yayi dai- dai da ranar Arafa, ko Ranar Ashura da makamantansu, Ma’anar (abinda aka Farlanta maku) ma’anarsa aka shar’anta, kuma aka sunnanta maku.