MARABA DA ZUWA SHAFINMU NA MUSULUNCI

29 Oct 2007

..... KE BATA ZUCIYA.....

Bismillahir Rahmanir Rahim
ABUBUWAN DA SUKE BATA ZUCIYA
Na: Imamu ibnul Qayyim
Imam ibnul Qayyim Allah yayi masa rahama yace: Amma abubuwan da suke bata zuciya guda biyar sune wanda yayi nuni akansu: yawan Cakud’a da mutane, da buri, da rataya da wani wanda ba Allah ba, da K’oshi, da barci. Wadannan sune manyan abubuwa guda biyar da suke bata zuciya.
NA FARKO: YAWAN CAKUDA DA MUTANE: Amma tasirin da yawan cakuda da jama’a yakeyi shine Zuciya zata cika da da Hyakin Numfashin Yan Adam har tayi bak’i, kuma hakan ze tilasta masa darewa da rabuwa da damuwa da bakin ciki,da rauni, da daukan abinda baze iya daukansa ba na takaicin Abokan banza, da bata abubuwan da zasu kawo masa amfani, da rafkana wato shagaltuwa daga barinsu, da wadansu al’amura, da kuma rarraba tunaninsa wajen nufinsu da nemansu, To menene yarage a wurinsa na ALLAH da ranar lahira?
* Wannan kenan, kuma dayawa daga cikin cakuda da mutane ya jawo bala’i, kuma yazama sanadin hana samun ni’ima, da saukar da Jarrabawa, da lalacewar dama, da musiba ta fad’o, kuma da aukuwan bala’i, kuma shin ba duk cutarwan dayake samun mutane ba, mutane ke zama sanadi?
* Kuma wannan cakuda da jama’an yana kasancewa ne wani nau’i ne na soyayya anan duniya, amma ze juye yazama Hukunci da gudun sashinsu daga sashi, idan kiyayya ta gaskiya ta tabbata, kuma me cakuda da jama’a ze cizi yatsa saboda nadama, kamar yanda Allah madaukakn Sarki yace: (“kuma a ranar da me zalunci yakeyin cizo akan hannayensa, yana me cewa: kaicona Inama da ace nabi tafarkin manzo! Ya kaicona! Inama! da ace ban riki wani masoyi ba! Tabbas, Hakika ya batar dani bayan tunatarwa tazo mini, kuma lallai Shed’an ya kasance ga mutum me zumbulewa.” Sur.Furqan 27-29) kuma madaukakin sarki yace: (Masoyan juna a wannan yinin, sashinsu mak’iyi ne ga sashe in banda masu tak’awa” (wato masu jin tsaoron Allah su masu san junane) Sur. zukhruf 67) kuma Badansa –wato Annabi Ibrahim- Yace: (“Babu abinda kukayi sedai kun riki gumaka saboda soyaiyar tsakaninku a cikin rayuwar duniya. Sa’an nan a ranar k’iyama sashinku ze kafirce ma sashi,kuma sashinku ze tsinewa (la’anta) sashi kuma makomarkun itace wuta, kuma Azzalumai basuda wadansu ma temaka” Sur. Ankabut 25)
* Kuma ma’auni me amfani a cikin cakudanya da jama’a: shine: yayi cakuda da mutane a cikin alkhairi, kamar Sallar juma’a da sallar Jam’i, da Iduka da Hajji, da koyan karatu da Jihadi, da yin Nasiha.
kuma ya kauracemasu a cikin aikata sharri, da halal din da baya da amfani.
* Idan bukata tasa shi haduwa da jama’a, ta yanda be sami daman kadaituwa daga garesu ba, to yaji tsoro kada ya goyi bayansu, kuma yayi hakuri akan cutarwan su, domin dole su cutar dashi, matukar beda karfi ko matemaki.
Sedai cutarwa ne da daukaka zata biyo bayansa, da soyayya agareshi, da girmamawa da yin yabo agareshi, daga wajen muminai da ubangijin halittu, kuma goyon bayansu kaskancine zebiyo bayansa da kiyyaiya gareshi, da Fushi da zargi daga wajensu, da muminai, daga ubangijin halittu. Saboda haka yin hakuri akan cutarwansu shine yafi alkhairi kuma yafi makoma me kyau, kuma yafi godiyan makoma.
* Kuma idan bukata tasa ya cakudu dasu a ckin halal da bashi da amfani, se yayi kokari ya juya wannan zaman yakoma yin biyyaiya ga ALLAH idan yasami dama.
NA BIYU: HAWA KAN TEKUN BURACE-BURACE:
Kuma shi kogine da beda tudu. Shi rafine wanda marasa rabo ke hawa daga cikin halittu, kaman yanda aka ce: guguwan burace – buracen karya, da tunanin banza, bazata gusheba, tana wasa da wanda ya hauta, kamar yadda karnuka ke wasa da gawan mamaci, kuma kaya ce na kowace rai, wulakantacciya kaskantacciya dake kasa, batada himman da za’a sami gaskiya da ita a fili, kai tasaba da burace –buracen kwakwalwa. Kuma kowanne da irin halinsa: daga me burin abin koyi da sarauta, da kuma Fatauci abayan kasa da zagaye – zagayen garuruwa, ko saboda dukiya da kudi, ko dan mata da yan samari, wanda yakeda burace – burace yana kama da wata sura da yake nema a cikin zuciyarsa wanda yasami rabo da samunsa, kuma yaji dadin samu rabo dashi, to yayin da yake a ckin wannan yanayi, se kawai yafarka se gashi akan tabarma!!
*To me himma datake babba, burace – buracensa sunna kewayawa ne a tsakanin da Ilimi da Imani, da yin aikin daze kusantashi zuwa ga Allah (Ubangijinsa) kuma ya matsar dashi zuwaga yin makwabtaka dashi. To burace – buracen wannan shine Imani da haske da hikma, amma burace –buracen wadancan zambace da rudu.
Kuma hakika manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yayi yabo akan masu yin buri na alkhairi, har ma yasanya ladan wanda yayin burin aikata aikin alkhairi kamar na wanda ya aikata din.
NA UKU: RATAYUWA DA WANDA BA ALLAH BA MADAUKAKIN SARKI: Kuma Wannan shine mafi girman abinda ke bata zuciaya kai tsaye, bashi da abinda yafi wannan cutarwa, kuma abinda yafi wannan yanke masa abubuwa masu amfani da tsira kamansa,domin idan har yaratayu da wanda ba Allah ba, Allah se ya dogarar dashi zuwa ga wannan abinda daya ratayu dashi, mutuwansa yasami abinda yakeso a wajen wanda ba Allah ba daya Ratayu dashi, da juyawarsa zuwa ga waninsa, shi din be sami rabonsa da yake wajen Allah ba, kuma be kai wajen abinda yake buri ba, da ya ratayu dashi. Allah madaukakin Sarki yace: (“kuma sun riki wadanda ba Allah ba (wato gumaka) a matsayin abin bauta don suzama matemaka a garesu, A’aha zasu kafircema ibadarsu, kuma su kasance mak’iya akansu” Sur. maryam 81 -82) kuma yace: (kuma sun riki wadansu abubuwan bautawa da ba Allah ba, sunyi tsammanin zasu temakesu. ( Bazasu taba iya temakonsu ba, alhali su din runduna ce daza’ akawosu (cikin wuta) Sur. Yasin 74 -75).
* Wanda yafi kowa kaskanci: shine wanda ya ratayu da wanda ba Allah ba, domi duk abinda yawuceshi na maslahohinsa da tsiransa da samun rabonsa, shine mafi girman abinda yasamu daga wanda ya rtayu dashi, shi yana fuskantar gushewa da kufcewa.
Kuma misalin wanda ya ratayu da wanda ba Allah kamar kwatankwacin wanda yake neman Inuwane daga zafi ko neman sanyi agidan gizo – gizo, mafi raunin gidaje.
* A dunkule: tushen shirka da K’a’idar da aka ginashi akanta: shine ratayuwa da waninda ba Allah ba. Kuma me yin hakan abin zargine kuma abin kaskanci, Allah madaukakin sarki yace: (“kada ka hada wani da Allah a wajen bauta, har kazauna kana abin zargi wulak’antacce” Sur. Isra’i -22) ma'anan abin zargi: bakada me gode maka, wulakantacce: kuma babu me temako agareka.
NA HUDU: ABINCI: Kuma abinci yana bata zuciya ta nau’i biyu:
Na d’aya: abinda ke bata zuciyan dakansa sune kaman abubuwan da’aka haramta. Kuma suma sun kasu kashi biyu: * Abubuwan da’aka haramta saboda Allah, kamar mushe, da Jini, danaman kare, da masuyatsu daga cikin dabbobi, da tsuntsaye masu k’unba. * Abubuwan da’aka haramta saboda bayi: kamar abinda aka sata,da wanda akayi kwacensa, da wanda akayi fashinsa, da duk wani abinda aka amsa a hannun meshi ba tareda izininsa ba, kodai fin karfi kokuma jin kunya da zargi.
Na biyu: Abinda ke bata wani sashi na zuciya kuma yawuce iyaka, kamar yin almubazaranci da abinda yake halal ne, da koshi wanda yawuce iyaka, domin ze hanashi yin abubuwan d’a a (biyaiya), kuma ya shagaltar dashi da cin abincin daze cika mai ciki sosai, yin kokari har se yasami hakan, kuma idan yasameshi, to ze hanashi (gudanarda hakan?) wato zesashi tumbi-da yin kariya daga abinda ze cutardashi, da cutuwa da nauyinsa, kuma abubuwan da sukesa sha’awa zasu yi k’arfi agareshi, kuma zebi hanyar shedan ya fadadata, domin yana gudu a jikin dan Adam kamar yadda jini ke gudu (yana bin hanyar jini ajikin dan adam). To Azumi kuma yana kuntatasu kuma ya yoshe hanyoyinsa, kuma duk wanda yaci abinci da yawa to ze sha ruwa da yawa, kuma zeyi barci me yawa kuma yayi asara me yawa. Kuma yazo cikin hadisi mashhuri: (“Dan Adam be cika mazubinsa- tumbinsa ba- da sharri fiyeda cikinsa, wasu y'an lomomi sun isa dan Adam wanda ze tsayu da doronsa ko bayansa. Idan kuma yakasance babu makawa, to daya bisa uku na abincinsa, daya bisa uku na abin shansa,daya bisa uku na numfashinsa,” Tirmidhi da Ahmad da Hakim)
NA BIYAR: YAWAN BARCI: Domin kashe zuciya,kuma yasa jiki yayi nauyi, kuma ya bata lokaci,kua nya gadar da yawan mantuwa, da kasala.
Kuma daga cikin barcin akwai wanda yake makaruhi ne (abinda aka kyamaci aikatashi) daga ciki akwai wanda yake cutarwa, wanda beda amfani da yake cutarda jiki, kuma barci mafi amfani: shine wanda akayishi lokacin tsananin bukatuwa zuwa gareshi. Da barcin Farkon dare, shine yafi amfani akan na karshensa,kuma barcin tsakiyar rana shi yafi amfani akan na farkonsa da na karshensa, kuma duk lokacin da barci yayi kusa da farkonsa ko karshensa, amfaninsa yana raguwa, kuma cutarwarsa yana karuwa, musamman ma dai barci da la’asar. Da barcin farkon rana sedai ga wanda beyi barci ba da daddare da yawa.
* Daga cikin makaruhinsa (barci) akwai: Yin barci tsakaicin sallar Asubahi da fitowar rana, domin lokacine da’ake samun Ganima (rabon arziki) kuma tafiya a wannan lokaci tanada fifiko me girma koda sun kasance sun kwana suna tafiya, ba'aso su tsaya a wannan lokacin har se rana ta fito, shine farkon Yini da mabudinsa, kuma lokacin saukowar arziki, da samun kaso, da saukar albarka. Kuma a cikinsa Yini ke farawa, kuma a lokacin ne ake janye hukuncin samun kason wannan yini. Saboda haka yakamata yin barci a cikinsa yazama ga wanda yazama masa dolene kawai wato kamar barcin wanda ya matsu.
* A dunkule matsakaicin barci da me anfaninsa shine,barcin a rabin lokacin dare na farko,da kuma karshensa, kuma shine kwatankwacin awa takwas. Kuma wannan shine mafi dacewar barci, kuma gwargwadan abinda ya karu akansa ko ya ragu, gwargwardan yadda zeyi tasiri a adabi’ance.
* Daga cikinsa akwai wanda beda amfani: shine yin barci a farkon dare, daf da faduwan rana har zuwa sanda duhun, Isha ze bace. Kuma Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yakasance yana kyamatarsa. To shi abin k’ine a shari’ance da kuma dabi’a. Allah ya temakemu.

6 Oct 2007

HUKUINCE HUKUNCEN SALLOLIN IDI (Karamar Sallah da Babba)ٍ

Dasunan Allah Mai Rahama Mai Jinkai

SALLOLIN IDI GUDA BIYU

Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya shar'anta ma bayinsa yin Iduka guga biyu, sallar Idi guda biyu, Sune Sallar Idi Karama da Idi Babba

HUKUNCIN YINSU

Halartar Sallar Idi dai Sunnah ce, wacce take mekarfi wato kamar wajibi take, saboda Allah madaukakin Sarki Yayi Umarni dasu inda Yace: (Lallai ne mu munyi maka kyauta mai yawa, saboda haka kayi Sallah domin Ubangijinka, kuma kayi suka –wato sukan rakumi ko yanka- kenan.) Sur, kauthar.1-2

Kuma ya rataya samun rabo da ita inda yace: (Hak'ik'a wanda ya tsarkaka (da imani) yasami babban rabo, kuma ya ambaci sunan ubangijinsa sannan yayi sallah.) Sur. A'ala 14-15

LOKUTAN YINSU

Shine lokacin da rana ta fito sama gwargwadon dagawan mashi daga k'asa har zuwa lokacin Gushewar rana (zawali) amma abinda akafiso shine ayi Idi babba a farkon lokaci, saboda mutane su samu daman yanka layyansu, Idi karama kuma anfiso a jinkirta ta saboda mutane su sami daman fitar da zakkan kono. Yatabbata manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Yana yin hakan a Hadisin Jundub Allah yakara yarda agareshi.

LADUBBANSU DA ABUBUWAN DA SUKE MUSTAHABBAI ACIKINSU

1. Yin Wanka da Sanya turare da Sanya mafi kyawun tufafi. Saboda fadin Anasa Allah Yakara Yarda Agareshi Yace: (Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Ya Umarci mu da mu sanya mafi sabunta abinda muka samu , kuma mu sanya mafi kyawun turare, kuma muyi layya da mafi tsada daga abinda muka samu-wato muke dashi) Imamul Hakim.

Tunatarwa: Amma ba'a sanya jajayen kaya biyu wato taguwa da wanda, ko me ruwan rawaya guda biyu, saboda manzan Allah ya hana sa wadannan launukan, amma babu laifi idan guda dayane

2.Cin Abinci kafin fita zuwa Sallar Idi K'arama, Ranar Idi Babba kuma se idan andawo daga Idi sannan se aci daga abin Layya, wato yanka da mutum yayi. Saboda Hadisin Buraidah Allahn Yakara masa Yarda Yace: (manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Yakasance Baya yin Sammako a Ranar Idi K'arama har se yaci, -wato se yaci wani abu- kuma bayaci a Ranar Idi Babba har se yadawo, se yaci daga abin Layyansa.) Imamut-Tirmidhi

3. Yin Kabbarori tun daga daren Idi Karama da Idi Babba, na Idi Karama za'a cigaba dayi lokacin fitowa daga gida zuwa filin Idi, baza'a yanke ba har se Liman Ya'iso, snnan a yanke. A idi Babba kuma za'a cigaba dayi har zuwa kwanaki uku na Shanyan Nama wato na Layya, Ga Lafazin Kabbarorin: Allahu Akbar Allahu Akbar La'ilaaha illallaah, Allahu Akbar Allahu Akbar, Walillaahil Hamd. Kuma an karfafa san yinsu a lokacin fitowa daga gida zuwa Filin Idi, da Bayan Sallolin Farilla guda biyar, a kwanakin Idi babba saboda fadinAllah Madaukakin Sarki: (kuma ku ambaci Allah a cikin wasu kwanaki k'ididdigaggu) Sur. Baqarah-203.

Da fadansa ( kuma ya ambaci sunan Ubangijinsa Kuma yayi Sallah)Sur. A'ala 15. da fadansa (..domin ku girmama Allah Saboda Shiriyar da yayi maku…) Sur. Alhajj-37.

4. Fita zuwa filin Sallar Idi ta wata Hanya da dawowa ta hanya ta dabam wato sauya hanya kenan Saboda manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Yakasance yana aikata hakan kamar yadda Jabir yafada acikin hadisi Allah Yakara masa yarda. Bukhari ya ruwaitoshi.

5. Yin Sallar Idi a fili, se dai idan an samu ruwan sama, ko makamancinsa to se ayi a cikin masallaci. hakan Yazo cikin Hadisi ingantacce.

6. Yima juna Barka ko Murna da Idi, da fadin: TAQABBALAL LAHU MINNA WA MINKUM saboda Sahabban Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam sun kasance in sun sauko Idi suna fadama junansu Haka idan suka hadu ( taqabbalal lahu minna wa minkum) Imamul Baihak'i. Ma'ana Allah Ya Karba Mana Idinmu tare danaku.

7. Rashin Yin Almubazzaranci a abinci da abin Sha, das wasa wanda aka halasta, saboda fadin manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam: ( Ranakun Idi ranaku ne na ci da sha, da ambaton Allah Madaukakin Sarki ) Imamu Ahmad.

SHIN KO ANA YIN NAFILA KAFIN IDI KO BAYANTA?

Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yayi hani da yin Salla kafin Idi ko Bayanta kuma ba'ayin kiran Sallar Idi ko tada Ik'ama, haka kuma Sahabbansa.

SAURAREN KHUDUBA

Anaso ga Wanda ya halarci Sallar Idi da yatsaya ya saurari Khuduba domin akwai lada acikin hakan, amma anyi rangwame ga wanda beso yaji da yatafi batareda yatsaya yayi surutu ga masu sauraro ba, kuma haka anyi rangwame ga wanda yayi Sallar Idi base ya halarci juma'a ba, wato idan Idi ta kasance ranar juma'a kenan.

Ya Allah ka sanya ayyukanmu suzama saboda kai kuma ka karba manasu Amin.

4 Oct 2007

Yin Azumin Sittu Shawwal

Azumin Sittu Shawwal

Imamu Muslim ya fitar da Hadisi ingantacce Daga Abu Ayyub Al'ansari Allah Yakara Yarda agareshi daga ManzanAllah Sallallahu Alaihi Wasallam Yace: (Duk Wanda ya Azumci Ramadan Sannan Y bishi da Azumi Shida a cikin Shawwal ya kasance kamar wanda ya Azumci shekara) Muslim.

Azumin kwana shida na watan sallah wato watan shawwal kenan Mustahabbine, wannan shine zancen mafiya yawa daga cikin malamai, wasu kuma sukace makaruhi ne saboda jin tsoron kada a dauka cewa shima wajibi ne kamar na Ramadan.

Yadda Ake Azumtansa

Malamai sunyi zantuka guda uku (3) kamar haka:

1. Yin Azumin guda shida ajare a farkon watan.

2. Yin Azumin ajere ko a rarrabe duka daya ne a kowani lokaci a cikin wata.

Fa'idan Azumin Shawwal

1. Yin Azumi Shida na Shawwal yana Cika ladan Azumin shekara.

2. Azumin Shawwal kamar Sallolin Nafiloli ne da'ake yi kafin da bayan Sallaolin farilla. Wanda suke cika nak'asa da tasamesu

2 Oct 2007

I'ITIKAFI

I'ITIKAFI

Dasunan Allah mai Rahama Mai Jinkai

Shine lazimtan masallaci da zama cikinsa da niyyan samun kusanci zuwa ga Allah. kuma malamai sunyi ittifak'I -wato sun hadu- akan cewa itikafi an shar'antashi kuma mustahabbi ne.

Tunatarwa: wasu mutane na kuskure ta yanda suke daukan cewa Itikafi, yakebanci manzan Allah ne Sallalahu Alaihi Wasallam shi kadai, wasu kuma suce hadisin Itikafi an shafe shi, wasu kuma suna dauka cewa Itikafi na dattawane ko akasin hakan, to duk wadannan kurakurai ne ba'a sha. Nana A'isha Allah yakara yarda agareta tace: (Lallai manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yakasance yanayin Itikafi a cikin goma na K'arshe na Ramadan har Allah yadauki ransa, sannan matansa sukayi Itikafi a bayansa) Bukhari. Ibn Hjar yace (Ba'a shafe hadisin ba kuma baya cikin abubuwan da suka kebanci ManzanAllah Sallallahu Alaihi Wasallam)fathul baari 4/272.

HUKUNCIN ITIKAFI

Mafi yawan malamai sun tafi akan cewa mustahabbi ne.

Imamu Malik Yace: (Nayi tunani akan al'amarin Itikafi, da abinda yazo akansa, da yanda musulmai suka barshi, tareda cewa manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam, be kasance yabarshi ba, se naga cewa sun barshi ne saboda yanada wahala akansu.)

Imam Azzuhri Yace: (akwai mamaki a Al'amarin musulmi! Sun bar Itikafi, tareda cewa Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam, be barshi ba tunda yazo Madinah , har Allah madaukakin Sarki yadauka ransa.)

SHARUDDAN ITIKAFI

1. MUSULUNCI: baya inganta ga wanda ba musulmi ba.

2. HANKALI: mahaukaci baya itikafi, saboda koda ibada ta wajibi bata zama dole akansu ba, andaga alkalami akansu.

3. NIYYA: sharad'I ce ga dukkan ibadodi, kuma duk aikmin da babu niyya a cikinsa ba karbabbe bane.

4. MASALLACI: ga namiji dolene yayi a masallaci, amma mace kuma anyi sabani akanta, Malam SUHNUNU Yace: (nace ma ibnul K'asim: menene zancen Imamu Malik gameda Itikafin mace tayi amasallacin jama'a? se yace Na'am, yace: a zancen Malik tayi Itikafi a masallacin gidanta? Se yace: Hakan baya burgeni, ana itikafi ne a masallacin da'aka yishi dan Allah.) Mudawwana 1/295.

Sheikh Aminul Hajj yace: (amma yafi rinjayen dalili awurina shine mace tayi Itikafinta a gidanta, wato wurin da takebance shi tana sallah a cikinsa.

5. AZUMI: wasu daga cikin malamai sukace kada mutum yayi itikafi face yaname Azumi, an tambayi Ibnul K'asim: (shin anayin itikafi batare da azumi ba a cikin zancen Malik? Se yace: ba'ayi se da Azumi. Wasu kuma sukace anayi koda mutum beyi Azumi ba, Sukace wannan shine ra'ayi mafi rinjayen dalili, saboda Hadisi Umar ingantacce da Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya Umarce shi da yayi itikafi yayin da yace masa yayi alwashin yin hakan a jahiliyya, kuma be ce masa yayi Azumi ba.

6. IZINI: dolene se miji yayi wa matarsa izini ko abinda ya mallaka na bawa ko baiwa, miji mace yana gida ne ko yayi tafiya dole tanemi izininsa, kuma idan yayi mata izini, to be kamata ya hanata ba kuma.

RUKUNNAN ITIKAFI

1. Zama a cikin Masallaci. 2. Nisantan Jima'I da abubuwan da zasu iya kaishi yin hakan. 3. Nisantar manyan laifuka. 4. Musulunci. 5. Hankali. 6. Tsarki daga Haila. Itikafi yana baci saboda rashin daya daga cikin wadannan.

ABUBUWAN DASUKE BATA ITIKAFI

1. FITA DAGA MASALLACI: baya halasta fita daga masallaci, In banda fita saboda: dan Biyan bukata kamar fitsari ko bayan gari, wankan janaba da na jumu'ah, cin abinci ko abin sha idan be iya ci ko sha a wurin da yake itikafi, idan yaji tsoron wuta ko sata kom rushewan gini, in aka fitar da shi da karfi, idan mace tayi haila da sharadin ta dawo da tayi tsarki, idan mijin mace yarasu ko yasake ta zata fita a mafi rinjayen zancen malamai biyu wasu sukace zata cigaba har seta kammala, fita saboda yin Umara, fita da mantuwa, idan yayi hauka ko suma.

2. YIN JIMA'I: saboda Allah yace: (kuma kada ku sadu dasu, alhalin kuna masu Itikafi a cikin masallatai…) Sur.Baqarah-186. haka sun bantan mace da sha'awa.

3. YIN RIDDA:wato fita daga musulunci

4. YIN MANYAN LAIFUKA: kamar yin zina da sata acikin itikafi, wanda mutane suna sakaci da daukan abin wani ko da kadan kuwa se a kiyaye.

5. YIN HAUKA KO SUMA: yana bata itikafi se dai idan yasami lafiya ko ya farfad'o to se yacigaba.

6. HAILA: idan mace tayi haila itikafinta ya baci, amma idan tayi tsarki se ta cigaba, na bayan be baciba.

ABUBUWAN DA BA'ASO GAME ITIKAFI

Ba'aso me itikafi ya shagaltu da abinda ba ambaton Allah ba, da kuma abinda ba dolene ba.

1. jayayya. 2. zagi damaganganun banza. 3. Yin giiba da Annamimanci. 4. Kallon abinda yake haramun. 5. Rashin yin magana gaba daya tun daga safe har dare da sunan bauta.

Tunatarwa: wasu daga cikin daliban ilimi se kaga suna zuwa itikafi da wasu littafai na karatunsu suna yin muraja'a, ba haramun bane amma kamata yayi tunda kwanakine yan kadan a cikin shekara, meze sa bazakayi hakuriba, sauran kwanakin shekara kayi acikinsu.

ABUBUWAN DASUKA HALASTA GAME ITIKAFI

1. Yin wanka da canza kaya, da sanya kayan da yakeso.

2. Cin Abinci da Shan Abin Sha a cikin masallaci.

3. Yin magan da yan uwa, amma ba'ason yawaita surutu da mutane.

4.Ya nemi Aure ko a daura masa Aure.

5. Yin Aski da yanke Farce.

6. Sanya turare.

ABUBUWAN DA SUKE MUSTAHABBI GA ME ITIKAFI

1. Mustahabbi ne ga me itikafi, yakafa tanti da ze kangeshi daga jama'a, inbe samu ba se ya lazimce wurin da babu jama'a ta yanda baze barshi ba seda larura.

2. kiyaye yin Sallah cikin jama'a, da nafiloli.

3. Yawan karatun alk'ur'ani, da rashin shagaltuwa da abinda ba ruwa.

4. Yawan ambaton Allah, zikiri, da tasbihi.

5. Yin azumi a cikin wantan da ba ramadan, ga wanda zeyi itikafi da rana.

6. Yawan yin kokari wajen d'a'a.

MAFI KARANCIN ITIKAFI DA MAFI YAWANSA

Itikafin neman lada baya da kad'an ko mafi yawa, se dai wanda yayi Itikafi a goman k'arshe na Azumin kada ya fita se idan anga watan Sallah wato Shawwal, malamai sun hadu akan cewa baya da mafi yawa, amma sunyi maganganu akan karancinsa, wasu sukace mafi karancinsa Sa'a, wasu sukace Yini daya da dare, wasu sukace kwana goma.

Imamul k'urtabi yace: ( mafi karancin itikafi a wajen Malik, da Abu Hanifa, dare da yini….)

YAUSHE AKE SHIGA ITIKAFI KUMA YAUSHE AKE FITA

A. Shiga wajen itikafi:akwai zancen malamai guda biyu:

1. Shiga bayan sallar Asubahin ranar Ashirin da d'aya na Ramadan, saboda hadisin Nana A'isha Allah yakara mata yarda tace: (Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam idan ze shiga itikafi yana yin sallar Asubahi, sannan se yashiga wurin itikafinsa) Bukhari. kuma wannan shine mafi rinjayen dalili. Kuma mazhabinAhmad da Laith da Ishak'.

2. Shiga kafin rana r daren Ashirin da d'aya ta fad'i, wannan shine mazhabin Malamai hud'u

B. Fita daga itikafi: Ana fita daga wurin itikafi bayan ganin watan sallah, wasu kuma sukace mustahabbine ya bari har yayi sallar idi sannan ya tafi.

SIRRIN DA YAKE CIKIN I'ITIKAFI

Bauta tana da sirruka da hikimomi masu yawa, saboda ayyuka gaba daya, makewayansu itace Zuciya, kamar yanda Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Yace (..Kusaurara! lallai acikin jiki akwai wata tsoka wanda idan ta gyaru, to dukkan sauran jiki ya gyaru, kuma idan ta bace, to dukkan Sauran jiki ya baci, ku saurara! Itace zuciya.) Bukhari da Muslim.

To in muka duba zamuga cewa mafi yawan abubuwan da suke bata zuciya, sune sha'awan cin abinci da abin sha da saduwa da Iyali da Zancen da ba na dole ba, da barcin da ba na dole ba, da abokai da basu da wata fa'ida da sauran abubuwa dasuke kawar da zuciya daga yin abinda yake biyayya ne ga Allah, se Allah ya Shar'anta wasu abubuwa na lada da zasukare zuciya daga rud'ani da shagaltuwa daga ambaton Allah, kamar Azumi wanda yake hana mutum cin abinci da abin Sha da Saduwa da Iyali da rana. To wannan hanuwan daga wadannan abubuwan jin dadi, shine yake karfafa alak'a tsakanin mutum da Ubangijinsa, da fuskantar dashi ga Lahira, kena Azumi garkuwa ce datake kare zuciya daga abubuwan sha'awa da suke kawar da mutum daga yin biyayya ga Allah, duk da hanine wanda yake matsakaici saboda an halasta wa mutum wadannan abubuwa a cikin dare.

To haka shima Itikafi yanada Sirri me girma, shine Kare mutum daga yawan cakud'a da jama'a, da yawan magana, saboda me Itikafi yana shagaltuwane da karatun Alk'ur'ani da Tsayuwa –wato yin sallah- da Zikiri da yawan yin Addu'a da makamantansu, haka kuma akwai kariya daga yawan barci, tunda yazo ibada ne ba barci ba, to wadannan abubuwa barinsu shike kara sa zuciya ta fuskanci Allah.

ABUBUWAN TUNATARWA

* Wasu daga cikin malamai sun tafi akan cewa ba'ayin Itikafi se a masallatai guda Uku kamar yadda yazo a cikin Hadisi, na hani akan yin Itikafi a masallatan da basuba, manzan Allah Sallalahu Alaihi Waasallam yace (Babu Itikafi face a masallatai guda uku) imamu Tahawi. -Wato masallacin Harami wato Ka'abah da masallacin Madinah da masallacin Aqsa wato Kudus-, Malamai suka fassara shi da cewa hani ne na yin alwashin yin Itikafi a wani masallaci da tafiya zuwa gareshi saboda hakan se a wadannan masallatan kadai ya halatta, ayi hakan saboda duk malaman mazhabobi Hud'u sun hadu akan cewa ya halatta ayi a kowani masallacin Juma'a.

* wasu sukan bar ayyukansu na wajibi saboda suyi Itikafi, to yin hakan kuskure ne saboda shi Itikafi sunna ce, saboda haka ba'a barin abinda yake wajibi saboda Sunnah.

Ya Allah Ka Karba mana dukkan Ayyukanmu a cikin Watan Ramadana kasa Muna cikin Bayinka Yantattu dag Wuta kuma kadatarmu da daren Lailatul K'adari. Amiin