MARABA DA ZUWA SHAFINMU NA MUSULUNCI

17 Jan 2008

ASHURA…… BIKIN SAMUN NASARA AKAN MASU DAGAWA.

ASHURA…… BIKIN SAMUN NASARA AKAN MASU DAGAWA.

Goma ga watan Muharram (Ashura ranace da Allah ya Girmama, kuma Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yayi bikinsa kuma yayi Umarni da Azumtansa, kuma yace gameda Ashura: Ashura wata ranace daga cikin ranakun Allah Madaukakin sarki, kuma wannan rana an kasance ana girmamata a lokacin jahiliyya, kuma yahudawa sun kasance suna daukansa a matsayin Idi, kuma shine Azumi na farko da’aka farlanta akan Musulmi kafin Ramadan.

Imamul Bukhari da Muslim sun ruwaito daga Abdullahi dan Abbas Allah ya k’ara yarda agaresu Yace:- “Yayinda Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasalllam Yazo Madina, ya sama yahudawa suna Azumtan Ranar Ashura, se Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Yace: “Ku bani labarin wannan rana da kuke Azumta, se Sukace: “wannan ran ace me girma Allah ya tseratar da Musa da Mutanensa a cikinta, kuma a cikinta y a halakar da Fir’auna da mutanensa se Annabi Musa yayi Azuminsa , a matsayin godiya ga Allah, saboda haka muma muke Azuminsa, se Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Yace: “To mu mukafi dacewa da Can- Canta da Musa akanku , se Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasllam Ya Azumcesa kuma yayi Umarni da’ayi Azuminsa”

Kuma gameda Falalar Azumin wannan rana Yazo a cikin Hadisi me tsawo cikin Sahihu Muslim daga Abu Qatada Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Yace:- “ kuma Azumin ranar Ashura Ina fatan Allah ya kankare zunuban shekara da ta gabata dashi”

kuma yazo cikin Sahihul Bukhari daga Abdullahi dan Abbas Allah Yakara masa yarda Yace: “Banga MAnzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya kebance wata rana da Azumi kuma yana Fifita Azuminsa akan waninsa ba se Azumin ranar Ashura , da wannan watan wato watan Ramadan.

Kuma sirrin dake cikin Azumin wannan rana shine: Nasara da Allah yabawa Annabi Musa da Mabiynsa da Halakar da Fir’auna da rundunarsa, wato biki ne Goyon baya da Allah yaba Muminai wanda sukayi Annabinsu biyayya kuma suka fita tareda shi domin su kafa wata kasa ta Musulunci sabuwa, kuma farin ciki ne da karya zalunci da dagawa dake tare da Fir’auna da rundunarsa wadandz suka yi dagawa a cikin garin Misra kuma suka yawaita barna a cikinisa.

Kuma Sirrin dake cikin rashin Can- Cantan Yahudawa da yin Bikinsa, da yin bikin Samun Nasara akan dagawa shine: Yahudawa sun shika cikin Ayarin masu Dagawa da Zalunci da girman kai, kai a yanzu ma sun zama sune Jagorin sa a duniya, saboda haka basu daceba da yin bikin wannan tunawan me girma. Saboda mu mukafi Can- Canta da Annabi Musa akansu, Mune masu yin Bikin, kuma muke da bam-bamci a bikin da yin Azumin Ran ta Goma da ta Tara ko ta Sha d’aya saboda mu sab’ama Yahudawa masu dagawa kamar yada Manzan Allah Salllallahu Alaihi Wasallam ya Umarcemu dashi.
BIKIN BAK’IN CIKI (TA'AZIYYA) NA Y’AN SHI’A RANAR ASHURA

Wannan hoton yanda Shi'a suke kunna kyandura kenan a daren Ashura irin Yanda kiristoci sukeyi.

BIKIN BAK’IN CIKI NA Y’AN SHI’A (TA'AZIYYA)

Amma gameda Ta’aziyyan Shi’a, babu wanda yake jayayya akan Falalan Husaini Allah Yakara yarda agareshi , da Darajojinsa domin ai yana daga cikin Malaman Sahabbai, kuma shugaba ne na Musulmai a duniya da Lahira wadanda aka sansu da Bauta da Jarumtaka da Yalwa… kuma shi d’ane wajen Y’ar mafificin halittu Sallallahu Alaihi Wasallam, itace mafificiya a cikin Y’ayansa, kuma abinda yafaru na kisansa Al’amarine abin k’i mummuna me bak’anta rai a wajen kowani Musulmi, kuma hakika Allah ya dauki fansa daga wanda suka kasheshi, Inda ya wulakantasu a duniya kuma ya sanya su suzama wa’azi, bala’o’I da fitinu suka samesu kuma kad’an ne suka tsira daga cikinsu, kuma me yasa bama ganin shugabanninsu suna zuwa suna Yanka jikinsu kamar yanda sauran mutane keyi ?

Kuma abinda ya kamata a lokacin tunawa da musiban kashe Husaini da makamancinta shine: Hakuri da Yarda da hukuncin Allah da k’addararsa kuma shi Allah yana zab’awa bawansa abinda yafi zama Alkhairi, Sannan Neman Lada wajen Allah madaukakin Sarki sakamakon Hakurin.

Amma be da Kyau ko kad’an abinda muke gani Shi’a na aikatawa na bayyana b’akin ciki da rashin hakuri wanda suka kirkiro kuma suka kallafa ma kansu, Mahaifinsa Aliyyu wanda yafishi Falala shima an kashe shi to meyasa basu rik’I mutuwarsa amatsayin abin ta’aziyya ba? kuma an kashe Usmanu da Umar kuma Abubakar yarasu Allah yakara masu yarda kuma dukkansu sun fishi falala… kuma shugaban Halittu Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallam ya rasu kuma ran mutuwansa ba’ayi abinda yake faruwa ba a ranar Kisan Hussaini, kuma yin bikin Bak’in ciki? Baya cikin Addini kai yafi kama da ayyukan Jahiliyya ( Alfatawa : Vol. 25 p. 307-314, da Iqtida’us siratal mustaqim Vol. 2 p.129 – 131.)

Imamu bin Rajab Yace gameda Ashura: Amma rik’onsa a matsayin Biki na Bak’in ciki, kamar yanda Rafidawa sukeyi, saboda kisan husaini Allah yakara yarda agaresu, yana daga cikin ayyukan wanda ya bata ayyukansa a duniya alhali yana tsammanin ya aikata aiki maia kyau, kuma Allah da Manzansa basuyi Umarni da rik’o da ranakun da Annabawa suka fuskanci Musiba da Ranakun Mutuwansu a matsayin Biki na Bak’in ciki, to yaya za’ayiwa wanda be kaisu ba, (Lata’iful Ma’arif P.113) kuma abin lura shine Matim na Rafidawqa a ranar Ashura baya da Alak’a da Musulunci a kusa ko a nesa, domin baya da alaka da Tseratar da Annabi Musa ko da Azumin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam, kai a fili yake ma sun musanya wannan Munasabar zuwa ga wani abu na daban, kuma wannan yan daga cikin Asalin Musanya Addinin Allah Madaukakin Sarki
Yaro kenan yake sarar kansa da Wuka ranar Ashura
Nan Suna dukan jikunansu ne da bulalan dalma
Dan K'aramin Yaro ma be tsira ba daga ta'addancin Bikin Bakin ciki na Y'an Shi'ah

Wannan Hoto na Yan Shi'ah Kenan Yanda suke yanka jikunansu a Ranar Ashura Shin wani irin Addini ne wannan?
Domin kagane ma idanunka hakan kana iya kallon talabijin ranar Ashura kaga yanda Y'an Shi'a a kasar Irak'i suke aikata wannan aikin saboda Akida dasuke da ita cewa dolene kowa yazubar da jininsa kamar yanda aka zubar da jinin Husaini Radiyallahu Anhu a wannan rana. To amma me yasa Mlumansu basa aikata hakan se akabar talakawa? Allah ya kiyayemu Amin

AYYUKAN MUTANE RANAR ASHURA A MA’AUNIN SHARI’AH

Wanda ke lura da al’amura ayau ze ga cewa suna kebance ranar Ashura da abubuwa masu yawa:- daga ciki akwai:-

* Azumi munyi bayanin matsayinsa a cikin Shari’ah,

* Akwai raya daren Ashura, da kwad'ayin kuntatama kai wajen yin abinci da yanka iri daban- daban na nama, da bayyanar da Murna da farin ciki.

* Akwai abubuwa dake faruwa a garuruwa daban- daban na ta’aziyya, da bak'in ciki ta hanyar aiwatar da wasu abubuwa na daban kamar yanda Rafidawa (Shia’a) sukeyi da wasunsu.

Yakamata musan matsayin wadannan ayyukan a shari'a, daganan suna iya zama ayyukan neman lada da kusanci zuwa ga Allah, ko kuma sanin rashin shar’antasu, se suzama bidi’ah da zasu nesanta mutum ga Allah.

To dolene mu sani cewa: ayyuka a wajen Allah basa samun karbuwa se sun cika wasu sharudda daga ciki akwai: Me yin aiki ya kasance yana me koyi da Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam, to idan muka duba ayyukan mutane a ranar Ashura sawa’un abubuwanda sukeyi a baya ko a wannan lokaci zamuga cewa suna da Nau’o’I daban daban:

1. akawai abinda yake na bauta : sun ware wwannan rana das wasu bauta na dabam kamar yin tsayuwa cikin daren Ashura, da ziyartan makabartu a cikinsa, da yin sadaka, da bada zakka, da karanta surorin da akwai ambaton Annabi Musa a cikinsu a alfijirin ranar Ashura… wannan da wasunsu, ayi abinda yasaba acikinsu wato dalilin yin aikin shine kebance shi da wani lokaci da Allah be ce a kebance su dayin hakan ba, kuma idan da Allah naso a aikata hakan to da yayi umarni da kwadaitar da yin hakan, kamar yanda ya kwaidaitar da yin Azumi a cikinsa.

To kenan an hana kebance wani lakaci da yin wata ibada ta daban, koda kuwa ace aikin shi karan kansa akwaishi a shar’aih wato ba'a haramtashi ba.

2. abinda yake Al’ada ce ake aikatawa, a ranar Ashura, irin wanda akeyi a Idi daga cikinsu akwai:-

* Yin wanka da sa kwalli da sanya turare da yalwata ma Iyalai a abinci da abin Sha da dafe dafe da toye- toye da yin yanka da bayyana Murna da farin ciki.

* kuma akwai wasu al’adu da suke cike da abin muni, kuma dukkan wadanna abubuwa sun samo asali ne a matsayin mayar da martani ga ta’aziyyan Rafidawa dasuke yi na nuna bakin ciki ga Mutuwan Husaini Allah yakara yarda agareshi, (To se Nasibawa sune wadanda suke nuna k’iyayya ga Ahlul baiti suke kishiyantan Shi’a wato rafidawa, wadanda su kuma suka wuce Iyaka wajen Ahlul baiti) da bayyana zagi garesu da nuna farin ciki, suka kirkiro abubuwan da babu su cikin Addini se suka fad’a cikin kamanceceniya da Yahudawa wajen daukansa a matsayin Idi wato biki kamar yanda ya gabata. (Kamar yanda Shaikhul Islam ya ambata a cikin littafinsa Iqtida’us siratal mustaqim Vol-2 p. 129-134).

* Yin Wanka kuma da sanya kwalli…..babu wani abu acikinsu da ya tabbata.

Imamu Bin Taimiyya yayi nuni ga Hadisan da sukazo dake nuna falalan Ashura yake cewa: dukkaninsu k’arya ce da’akayi wa Manzan Allah, babu wani abu daya inganta a cikinsa in banda Azumi, kuma wannan shine tafarkin Manzan Allah Sallalllahu Alaihi Wasallam.

Allah Madaukakin Sarki yace: "Hakika koyi me kyau ya kasance agareku daga Manzan Allah, ga wanda yake fatan Allah da Rana ta K’arshe kuma ya( ambaci Allah da yawa” Sur. Al-Ahzab -12.

kuma dayawa daga cikin wadannan da suke shagaltuwa da bidi’o’I, dayawa bin ManzanAllah Sallallahu Alaihi Wasallam na wuce su da bin aiki da Sunnarsa.

13 Jan 2008

HANYOYIN TABBATUWA AKAN ADDININ ALLAH (1) Bismillahir Rahmanir Rahim

Dukkan Yabo da Godiya sun tabbata ga Allah, Muna gode masa, muna Neman temako agaresa, kuma muna Neman Gafararsa, kuma muna Neman tsarin Allah da yakare mu daga sharrun kawananmu da Munanan ayyukanmu, Duk wanda Allah ya shiryar , to babu me batar dashi kuma duk wanda Allah ya batar to babu me shiiryar dashi, kuma Ina shaidawa Babu abinda ya Can-Canci bauta se Allah shi kadai baya da Abokihjn tarayya , kuma Ina Shaidawa Lallai Annabi Muhammadu Bawansa ne kuma Manzansa.

Bayan Haka: Tabbatuwa akan Addinin Allah abune da’ake nema wajen kowani musulmi na gaske da yake neman Tafarki Madaidaici tare da Himma da Shiriya.

Kuma wannan Maudu’in yanada muhimmancin saboda:

* Halin da Musulmi suke rayuwa a ciki a Yau da Nau’I daban- daban na fitintinu da abubuwan rud’i wanda da wutanta suke neman magani, da kuma dangogin Abubuwan Sha’awa da Shubuhohi wanda ta dalilinsu ne musulunci ya wayi gari yana bak’o , se wadanda sukayi riko dashi suka zama kamar yanda karin magana ke cewa: “Wanda yake riko da Addininsa kamar wanda ke riko ne da garwashin wuta”.

To babu shakka, duk me Hankali zega, cewa bukatan Musulmi a Yau, zuwaga Hanyoyin tabbatuwa tafi bukatan da dan Uwansa yake da’ita a lokacin Magabata, kuma kokarin daza’ayi wajen samun hakan shi yafi girma saboda yanda zamani ya lalace, da karancin na kwarai, da raunin matemaki da karancin masu temakawa.

* Yin ridda da komawa kafirci da juyewa yayi yawa, har hakan yasa wasu da sukewa Addini aiki suke jima musulmi tsoro ga makomansa kuma suke nema masa Hanyoyin tabbatuwa domin ya kaiga tsira.

* Batun yana daure da zuciya wanda Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Yace: “Wallahi zuciyar dan Adam tafi juyewa da tukunya idan ta tafasa” Ahmad da Hakim.

Kuma Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya buga wani misalin gameda zuciya Yace: “An sanyawa zuciya suna ne saboda juyawanta, lallai misalin zuciya kamar misalin ………ganye ko iri…. A Bishiya iska na kad'a cikinsa da wajansa” Ahmad.

To tabbatatar da wannan abinda yake jujjuyawa da guguwan Sha’awowi da Shubuhohi al’amarine da yake da hatsari , yana bukatan Hanyoyi masu karfi dazasuyi dai-dai da girman aikin da wahalarsa.

HANYOYIN TABBATUWA

Yana daga cikin Falalar Allah akanmu, da ya bayyana mana hanyoyi masu yawa na tabbatuwa akan Addininsa , a cikin littafinsa da kuma ta harshen Manzansa da Tarihin rayuwarsa, Sallallahu Alaihi wasallam.

Me Karatu zan bijiro maka da wasu daga cikinsu Kamar Haka:-

NA FARKO: FUSKANTAR ALQUR’ANI:

Alqur’ani me girma shine hanya ta farko na tabbatuwa, shine Igiyar Allah me karfi , shine Haske mabayyani , duk wanda yayi riko dashi Allah ze kareshi , wanda duk ya bishi to Allah ze tseratar dashi, kuma duk wanda yayi kira zuwa gareshi, za’a shiryar dashi zuwa tafarki madaidaici.

Allah madaukakin Sarki ya bayyana kololuwan manufar da tasa ya saukar da Alqur’ani a rarrabe, itace Tabbatuwa, Allah Madaukakin Sarki yace wajen mayar da martani ga Shubuhan kafirai: ( Kuma wadanda suka Kafirce suke cewa Inama da ace an saukar masa da Alqur’ani jimla guda ? Munyi hakan ne domin mu tabbatar dashi a zuciyarka, kuma mun jeranta karantashi da hankali jerantawa * kuma bazasu zo maka da wani misali ba , Face mun zo maka da gaskiya da kuma mafi kyawun fassara) Sur. Furqaan: 32-33.

Me Yasa Alqur’ani yazama Masdar wato tushen Tabbatuwa?

** Domin ya shuka Imani kuma ya tsarkake rai ta hanyar sadar da’ita da Allah.

**Domin wannan Ayoyin suna saukar da Sanyi da Aminci akan zuciyan Mumini, Guguwar fitina bazata share shi ba, kuma zuciyarsa zata natsu da ambaton Allah.

**Domin yana kara wa Musulmi tunani da Halaye na kwarai wanda dasu ne ze iya yima abinda ke kewayensa hukunci, to haka kuma ze bashi Ma’auni daze temaka masa wajen yima al’amura hukunci kuma hukuncinsa bazeyi rawaba, kuma zantukansa bazasu dinga war-ware juna ba saboda sabanin abubuwan dake faruwa ko mutane.

**Saboda yana mayar da martani ga Shubuhohi (wato abubuwa masu kama da gaskiya) da makiya musulunci suke samardasu daga wajen kafurai da Munafukai, kamar Misali me rai da Yan zamanin farko suka rayu dashi, wannan sune Misalan:

-Menene tasirin Fadin Allah Madaukakin Sarki: (Ubangijinka beyi ban kwana da kai ba kuma be kauracema ba -wato be k'ika ba-) Sur. Duha-3.

a cikin ran Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam lokacin da Kuraishawa sukace: “Anyiwa Manzan Allah ban kwana….”?

-Menene tasirin Fadin Allah Madaukakin Sarki: ( Harshen dasuke karkata zance dashi ba Ajame ne , kuma wannan Harshe ne na balarabe Mabyyani) Sur. Nahl-103. lokacin da Kuraishawa sukayi Ikirarin cewa wani mutum ne yake karantar da Annabi Sallallahu Alihi Wasallam Alkur’ani, kuma yana koyon Alkur’ani ne daga wajen wani kafinta ba rume a Makkah?

-Menene tasirin Fadin Allah Madaukakin Sarki: ( Ku saurara! A ciki fitiana suka fad'o) Sur. Tauba -49. a cikin zukatan Muminai lokacin da Munafukai sukace: Kayi man……”?.

Shin ba tabbatarwa bane akan tabbatarwa, kuma da daure zukatan Muminai, da kuam mayar da martani ga Shubuhohi, da kuma shiruntar da Masu bata?... ina rantsuwa da Ubangiji na Hakane.

Kuma yana daga abun mamaki, cewa Allah yayi wa Muminai Alkawari da samun Ganima me yawa bayan sun dawo daga Hudaibiyya -itace Ganiman Khaibara- dacewa kuma ze gagauto masu da ita kuma sune zasu sameta ba wasunsu ba, kuma Munafukai zasu ce zasu raka su, kuma Musulmi zasu ce bazaku tab’a binmu ba, kuma zasu cije se sun sauya maganar Allah, kuma zasu ce wa Muminai kawai kunayi mana Hassada ce, kuma Allah yabasu Amsa da cewa

( Sun kasance basa iya Fahimta se Y’an kad’an) Sur. AlFathi-15.

Sannan kuma Alk’ur’ani yabada wannan Labarin gaba dayansa ga Muminai Lokaci- zuwa Lokaci Mataki – Mataki, Kalma da Kalam.

To a nan zamu riski bam-bamcin dake tsakanin wadanda suka had’a rayuwansu suka daureta da Alk’ur’ani, kuma suka Fuskanceshi suna karantashi, suna Haddace shi, suna Karanta Fassaran shi-wato Tafsirinsa-, suna Yin Tadabburinsa –wato Yin Tunani acikin ayoyinsa-,da Umarnin Alk’ur’ani suke aikata komai, kuma gareshi suke komowa, da Wanda ya sanya zantukan dan Adam sunesukafi damunshi da abinda yake shagaltar dashi. Ya Kaicon wadanda suke Neman Ilimi suna ba Alk’ur’ani da Tafsirinsa kaso me yawa na laokutansu na Karatu. Akwai cigabansa nan gaba insha Allahu a kashi na biyu.

2 Jan 2008

TARE DA MANZAN ALLAH SALLALLAHU ALAIHI WASALLAM NA (2)

SUNA DA DANGANTAKAN MANZAN ALLAH SALLALLAHU ALAIHI WASALLAM

1. Allah Madaukakin Sarki Yace:- ( Muhammadu Manzan Allah ne ..)Sur. Fathi -29.

2. Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasllam Yace: ( Ina da Sunaye guda biyar : Nine Muhammad , kuma Nine Ahmad, kuma Nine Maahi -wato ma’ana me shafewa -, wanda Allah yake shafe kafirci dani, kuma Nine Alhashir -wato ma’ana me tara jama’a.-, wandaza’a tara mun mutane a gaba na, kuma Nine Al’aqib-wato ma’ana na K’arshe.-, wanda a bayansa babu wani Annabi) Bukhari da Muslim.

* Kuma Allah Yayi masa suna da Ra’uf -wato ma’ana me matuk’ar tausayi- da Rahim -wato ma’ana me Jinkai-

3. Kuma Manzan Allah Yakasance yana ambata mana Sunayensa se yace: ( “Nine Muhammad Nine Ahmad, Nine Almuqaffa, Nine Alhashir. Kuma Nine Annabin Tuba, kuma Nine Annabin Rahama”). Muslim

4. Kuma Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasllam Yace: ( “ Shin be isheku ba yazama abin Mamaki, yanda Allah yake kawar mun da zagin K’uraishawa da La’antansu? Suna zagina da Muzammam, kuma suna la’anta na da muzammam, Alhali kuwa Ni Muhammad ne”) Bukhari.

Ma’noni: Muzammam abin zargi.

5. Kuma Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasllam Yace: ( “ Lallai Allah Yazabi Kinana daga Y’ay’an Annabi Isma’il, Kuma yazab’i K’uraishawa daga Y’ay’an Kinana, kuma yazab’i Banu Hashim daga K’uraishawa, kuma yazab’eni daga Banu Hashim”). Imam Muslim

6. Kuma Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasllam Yace: ( “Kusnaya Sunayena, amma kada ku sanya Alkunyata, domin ni meyin rabo ne a tsakaninku”). Muslim.