MARABA DA ZUWA SHAFINMU NA MUSULUNCI

26 Aug 2007

Falalar Ramadan

Falalar Azumin watan Ramaadan Hadisi tabbatacce yazo cikin bukhari da muslim daga Abu Hurairah Allah yakara masa yarda yace"Manzan Allah Sallalahu Alaihi Wasallam Yace (Dukkan aikin dfa dan Adam yayi to nasane Duk aikin lada yanada guda goma makamancinsa, har zuwa a ninka masa sau dari bakwai,se Allah madaukakin Sarki yace: banda Azumi domin shi nawane kuma nine zansaka akansa, shi me Azumi yakame daga Sha'awarsa da abinci da abin sha saboda ni, me Azumi yanada Farin ciki guda biyu: farin ciki a lokacin daze sha ruwa da farin ciki lokacin gamuwa da ubangijinsa, kuma tabbas warin bakin me Azumi shi yafi dadi a wurin Allah akan Kanshin turaren Almiski). Allah ya kebance Azumi a wannan riwaya daga cikin ayyukan daake rubanyawa daga goma har zuwa dari bakwai saboda Azumi baya da adadi wajen Rubanyawa Allah shi yasan Adadin daze rubanyashi, domin shi Azumi yana daga cikin hakuri, Allah madukakin Sarki yace: ("Lallai Allah yana cikawa masu Hakuri ladansu ne batare da Iyakancewa ba"Sur. Zumar-10) kuma yazo cikin hadisi manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ma'anar Fadansa (Azumi nawane) ya jingina Azumi zuwa gareshi ne saboda acikin azumi akwai hana rai abinda aka haliccieta da