MARABA DA ZUWA SHAFINMU NA MUSULUNCI

6 Aug 2007

Shi yasa aka fifitasu....

Dasunan Allah mai Rahama mai Jinkai WADANSU ABUBUWA DA'AKA KEBANCE AL'UMMAR MUSULMI DASU AKAN SAURAN AL'UMMU Hakika Allah madaukakin Sarki ya karrama A'ummar musulunci, kuma ya daukakata akan sauran al'ummu, ya kebanceta da wasu abubuwa, ita kadai. Tabbas tasami wannan girmane, saboda daraja da falalan Annabinta Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallam, da imani datayi dashi. Daga cikin daukakashi da Allah yayi bayan yazabeshi daga cikin halittu,ya zaba masa Abokai (wato sahabbai) matemaka agareshi. Allah madaukakain Sarki yace ( "shine wanda yazabeku –sahabbai- kuma be sanya maku wani abu me wahala acikin Addini ba" ) (Sur. Hajji -78.) kuma yace ( "kuma haka muka sanyaku Al'umma mafificiya domin kuzamo masu sheda ga mutane (Annabawan dasuka gabata akan mutanensu) kuma manzo yazama me shesa akanku….") Sur. Baqarah-143). Saboda haka ne yazama dole akan muslmai dasusan abinda suke ciki na ni'ima,da kuma abinda suke akai na alkhairi, don suyi rikoda shi kumasuyi rikodashi kuma suyi aiki domin yadashi……………………….zamu cigaba insha Allah