MARABA DA ZUWA SHAFINMU NA MUSULUNCI

4 Aug 2007

MATSAYIN SALLAH

Dasunan Allah Mai Rahama Mai Jinkaiِ
SALLAH
Ita Dayace daga cikin rukunnan musulunci guda biyar, wanda Allah maduakakin sarki ya wajabtata guda Hamsin(50) yayin da manzan Allah Sallallaahu Alaihi Wasallama yaje Mi'iraaji (wato Sama) yakarbo ta yayi ta neman ubangiji da ya ragemana ita har aka rageta zuwa guda biyar (5) kamar yadda take a yau saboda tausayin manzan Allah garemu Sallalahu Alaihi Wasallam. Kuma manzan Allahn Sallalahun Alaihi Wasallam yace "Itace farkon abinda za'ayi Wa bawa sakamako (hisabi) Ranar k'iyama Idan tayi kyau dukkan Sauran aiki zasuyi kyau bawa yasama tsira kuma idan tayi muni to dukkan sauran ayyuka bazasu amfane bawaba. Sannan kafin Sallar da bawa yakeyi tasami karbuwa se idan tadace da yadda manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallama yayita kuma ya karantar domin fadan Ma'aiki "Kuyi Sallah Kamar yadda kuka ina yin Sallah", Sannan an wajabta yinta acikin jama'a (wato Jam'i a masallaci). Kuma wanda duk yabarta to yabar musulunci kamar yadda ma'aiki Tsira da Amincin Allah su kara Tabbata Agareshi yace " Alkawarin dake tsakaninmu dasu shine Sallah duk wanda yabarta to ya kafirta". To idankowannan shine al'amarin Sallah to yazama dole akan kowane muslmi dayasan mecece Sallah? Kuma menene Hukunce-Hukuncenta? da abubuwan dasu batata domin ta kasancce karbabaiya a wajen Allah Madaukakin Sarki…………….