MARABA DA ZUWA SHAFINMU NA MUSULUNCI

31 Dec 2007

TARE DA MANZAN ALLAH SALLALLAHU ALAIHI WASALLAM NA (1)

HAIHUWAR MANZAN ALLAH SALLALLAHU ALAIHI WASALLAM

1. Allah Madaukakin Sarki Yace:. ( Hakika Allah yayi baiwa akan Muminai da ya aiko da manzo daga cikinsu, yana karanta masu Ayoyinsa, kuma yana tsarkakesu, kuma yana karantar dasu Littafi -wato Alk'ur'ani da Hikma -watom Hadisi, duk da sun kasance kafin hakan suna cikin bata a bayyane) S. Al'imaran-164.

2. kuma madaukakin Sarki yace: ( kace masu nifa mutum ne kamanku, anayimini wahayi cewa tabbas mahaliccinku shine ubangiji guda daya) S. kahf-11.

3. An tambayi Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam gameda Yin Azumin Ranar Litinin?

Yace: " wannan rana ce da'aka haifeni a cikinta, kuma a cikinta aka aikoni, kuma a cikinta aka saukar min da Alk'ur'ani" Muslim

4. Hakika an haifi Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam a Ranar Litinin cikin watan Rabi'ul Awwal a Makka, a shekaran Fil- wato Giwa. shekara ta 571 C.E. daga Iyaye biyu sanannu: Mahaifinsa shine ABDULLAHI dan Abdulmutallib, Mahaifiyarsa kuma itace AMINA yar Wahabu, kakansa yarada masa suna MUHAMMAD Sallallahu Alaihi Wasallam, kuma Mahaifinsa ya rasu kafin Haihuwarsa.

5. Lallai Yana daga cikin Abubuwan dasuke wajibi akan Musulmai shine su san darajan wannan Manzo me girma, kuma suyi hukunci da Alkur'ani da'aka saukar masa, kuma su dabi'antu da halayensa kuma su bada kokari wajen kira zuwaga Tauhidi-kadaita Allah- wanda akansa yafara...........................me bin Umarnin Allah Madaukakin Sarki: ( Kace ina kira zuwaga Ubangijina kuma bazana hadashi da kowa ba cikin bauta). Sur.Aljinn-20.

18 Dec 2007

LAYYA

16 Dec 2007

YANKAN LAYYA BA'A GARIN ME LAYYA BA

TAMBAYA: Mu muna zaune a wani Gari, kuma Mahaifiyata da Y'an Uwana suna yanka wani adadi na Layya a kowace shekara, Ni kuma inaso in aikawa da Kawuna da kudin abin Layya na , don yasaya yayi min yankan, saboda halin talauci da suke a ciki, kuma shi kawuna yana zaune a wani gari ne da ban, shin ko zaku bani shawara gameda haka, koko inyi layya na a garin danake zaune, kuma wanne ne yafi falala? tunda ni zan wakilta wani ne da yayi min yankan, kuma bazanga dabban ba yayin da'ake yankata. MAI BADA AMSA: Prof. Dr. Sa'ud bn Abdullah Alfunaisan. Tsohon shugaban Faculty of Shari'ah, Imam Muhammad Bn Sa'ud University Riyadh. RANA: 05-12-1428 A.H. AMSA: Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah, Tsira da Aminci su Kara tabbata ga Manzan Allah. Bayan Haka: Ya Halarta ka wakilta Kawun ka dayake wani gari da kabashi kudin yasaya kuma yayi maka yanka, saboda ita dai Layya, sunna ce me karfi, wasu kuma sukace wajibi ce ga wanda yake da hali, kuma kallon yankan da kuma cin naman abin layyan, sunna ce ba wajibi ba, musamman kuma tunda Iyalanka zasu yi layyan, kuma abin layya guda daya yana isarma mutum da iyalan gidansa koda suna da yawa, kuma kamar yadda ka bayi bayanin halin da kawunka yake ciki wato yafi iyalanka bukata, saboda haka inka bashi kudin layyan yana wata kasa yayi maka, yahalarta a cikin Shari'a. Allah shine mafi sani.

11 Dec 2007

HAJJI DAI FARKO

Ni Babban ma'aikaci ne kuma me tarbiyya, Alhamdu Lillah Bani da gidana nakaina, ina haya ne, kuma ina da kudin da baze isheni sayen gida ba amma ze ishe ni yin aikin Hajji. shin zan sauke faralin Hajji ne tareda cewa ina haya? shin kuma ya halarta agareni da in jinkirta yin Hajjin har se nase gida, tare da cewa wannan hakan ze dauki shekaru masu yawa? Daga: Shafin: www.islamtoday.com/questions Malami me Amsa: Al'allama Ustaz Dr. Abdullahi bn mahfuuz bn biih, tsohon Ministan ma'aikatan Shari'a ta kasar Mauritania. Rana: 01-12-1428 A.H. Amsa: Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah, Tsira da aminci su tabbata ga Manzan Allah. bayan haka Wajibine gareka yakai dan'uwa da kaga batar da wajabcin Hajji, domin shi wajibine da baayin jinkiri a cikinsa, kamar yanda da yawa daga cikin Malamai suka tafi akai, to tunda kanada kudi daze ishekan yin aikin Hajji, kuma bazaka bar iyalanka ba a cikin kunci, toyazama dole akanka katafi kayi aikin Hajji kada ka jinkirta shi, domin Hajji wajibi ne, wanda ba'a jinkirta shi, kasmar yanda Imamu Malik da Imamu Ahmad suka tafi akan haka, kuma zance ne me k'arfi a wajen Hanafiyya.

9 Dec 2007

SUMBANTAN KA'ABA?

DAGA: Shafin: www.meshkat.net TAMBAYA: Shin Yana daga cikin Sunnah Sumbantan Ka'aba? MAI BADA AMSA: Sheikh Dr. Abdul-Hayyi Yusuf. Limamin Masallacin Jum'a dake Hayyud dauha, a Khartoum kuma Shugaban Sashin Thaqaful-Islamiyyah a Khartoum University a kasar Sudan. Dukkan Godiya ta tabbata ga Allah Shi kad'ai, kuma Tsira da Amincin Allah su kara tabbata ga wanda babu wani Annabi a bayansa, da Alayensa da Sahabbansa baki daya. Bayan Haka: Abinda yake Sunna dai, Shine sumbantan Hajarul Aswad da Ruknul Yamaani, kuma baya daga cikin Sunnah sumbantan wani abu wanda ba su ba, kamar ka'aba Allah yakara mata, kuma Sahabi Abdullahi dan Abbas Allah yakara masa Yarda, yayi inkari - wato ya nuna kyamarsa ga wanda ya sumbanci wani abu wanda ba Ruknai guda biyu ba- wato wanda aka ambanta-. Allah shine mafi sani.

29 Nov 2007

ABUBUWAN HANI A CIKIN HAJJI

ABUBUWAN DA AKA HARAMTASU GA MAHAJJACI

Duk wanda yayi Harama da Hajji ko Umurah an haramta masa, abubuwan da suke zuwa: 1.Rufe kai ga na miji, domin haramarsa itace bude kai, haka kuma Rufe fuska da Hannaye ga mace, domin haramarta itace budesu, sedai idan zata wuce maza, to seta rufe fuska. Kuma idan daya daga cikinsu yarasu, to za’a rufeshi a cikin haraminsa, se abude fuskar maace, kuma a bude kan na miji, kuma baza’a samasa turare ba.

2. Aske gashin kai ga na miji.

3.Yanke kumba.

4. Sanya Turare, sedai abinda yake a tufafinsa, wanda yayi harami dashi to babu laifi akansa.

5.Sanya tufafi dunkakke.

6. yin Jima’I da abubuwan dasuke haifar dayinsa.

7. Yin farautan wani abu, ko temaka ma meyin hakan, ko cin abinda akayi farautarsa.

8. Yayi tad’i wato neman aure, ko daura masa aure, ko aurarwa waninsa, ko ya halarci daurin auren waninsa.

WAR-WARE AIKIN HAJJI KARAMA DA BABBA

Mahajjaci yanada war-wara guda biyu: Karama shine bayan jifan jamratul ak’aba –wato shedan babba- a ranar Idi kenan, to daga nan komai ya halatta ga mahajjaci hatta saduwa da Iyali. da kuma War-wara babba, wanda yake bayan dawafin Ifada.

FIDIYA GA WANDA YA AIKATA ABINDA AKA HARAMTA

Duk wanda ya aikata daya daga cikin abubuwa guda biyar na farko da’aka haramta masa, da gangan –wato-yana sane bada mantuwa ba- to akwai fidiya akansa, kuma yanada zabi a cikin hakan, kodai ya yanka dabba, ko ya ciyarda Miskinai guda shida, ko yayi Azumin kwana uku (3) a duk inda yaso. Saboda faden Manzan Allah Sallalahu Alaihi Wasallam ga Ka’ab dan Ujratu Allah yakara masa yarda: …………………………………………………

AIKIN HAJJI

Menene Ma'anar Hajji? Hajji a harshen larabci ma'anarsa itace nufi ko aiki da yake zuwa lokaci zuwa lokaci. Amma a musulunci, idan akace hajji shine Nufin dakin Allah me alfarma domin aiwatar da wasu ayyuka kebantattu da Alalh madaukakin sarki ya ambata acikin littafinsa kuma Hadisai sukayi bayani akansu.

HUKUNCIN AIKIN HAJJI

Yin aikinHajji wajibine akan kowani musulmi na miji da musulma mace dasuke da iko. Kuma aikin Hajji ya tabbata acikin Littafi da Hadisi da Ijma'i.

Daga cikin Littafi : Allah madaukakin Sarki Yace: ( kuma lallai Allah ya wajabta wa mutane yin Hajjin dakinsa ga wanda yasami iko,kuma duk wanda ya kafirce to lallai Allah mawadaci ne ga Halittu.) Sur. Al'imrana

Daga Hadisi : Abdullahi dan Umar ya ruwaito Hadisi daga Mnazan ALLAH Sallalllahu Alaihi Wasallam yace: ( An gina musulunci ne akan abubuwa guda biyar : Shaidawa babu abin bautawa da can canta se Allah kuma Annabi Muhammadu Manzan Allah ne,Tsayar da Sllah, Bayar da Zakkah, Yin Hajji da kuma Azumin Watan Ramadana) Bukhari da muslim.

Daga Ijmaa'I : Dukkan Musulmai sun hadu akan wajabcinshi kuma dayane daga cikin rukunnan musulunci, kuma abune da kowa yasanshi acikin Addini, kuma duk wanda yyi musunsa to ya kafirta kuma yaayi rudda daga musulunci, haka kuma malamai sun hadu akan cewa aikin Hajji baya wajaba face sau d'aya a rayuwar mutum se dai idan mutum musulmi yayi bakancensa wato alwashi to yazama dole ya cika alwashinsa, amma duk abinda yayi bayan wannan to neman lada ne kawai.

Abdullhi dan Abbabs Allah yakara yarda agareshi yace Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yayi mana Khud'uba, se yace: (Yaku mautane Allah ya wajabta aikin Hajji akanku ) se Ak'ra'a bin Habis yace "Shin kowace shekarane ya manzan Allah? Se yayi shiru har se da ya maiamaita hakan sau Uku, sannan Manzan Allah Sallallahu Alaihin Wasalllam yace : ( da'ace nace E da yazama wajibi, kuma da dayazama wajibi bazaku yiba kuma bazku iyaba, Hajji sau dayane duk wanda yakara to neman ladane ) Ahmad, Abu dawud da Nasa'i.

FALALAR AIKIN HAJJI

Allah ya kwadaitar damu yin aikin hajji kuma ya bayyana d'umbin ladar da za'a samu a sakamakon hakan hadisan dasuke zuwa zasu bayyana haka:

Fadin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam : ( Duk wanda yayi Hajji, be yi rafasu ba -wato Jima'i a cikinsaba- kuma beyi fasikanciba –sab'on Allah- ze koma mara laifi kamar randa mahaifiyarsa ta haifeshi ) Bukhari da Muslim.

Fadin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam : (Yin aikin Umurah zuwa Umurah ana kankare zunubbai dake tsakaninsu, shiko aikin Hajji karbabbe baya da sakamako se Aljanna.) Bukhari da muslim.

Fadin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam : yayinda aka tambayeshi gameda mafificin ayyuka se yace " Imani da Allah da manzansa" akace seme kuma? Yace "se jihadi dan daukaka kalmar Allah" akace se me kuma? Yace" se aikin Hajji karbabbe". Bukhari da Muslim.

Fadin Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam………………..

SHARUDDAN WAJABCIN HAJJI

Seda sharudda masu zuwa hajji yake zama wajibi:

1. Musulunci

2. Balaga

3. Hankali: wato yakasance me hankali domin Hajji baya wajaba akan mahaukaci.

4. Y'anci: wato yazama d'a,domin hajji baya zama wajibi akan bawa. Dalilan wadannan sun gabata a cikin rukunin Azumi.

5. Samun iko: kamar yadda Allah madaukakin Sarki yace ( kuma lallai Allah ya wajabta wa mutane yin Hajjin dakinsa ga wanda yasami iko….) Sur. al'imrana -97.

RUKUNNAN HAJJI

Rukunnan Hajji guda hudune(4): Yin harama, Tsayuwa a Arafah, Yin d'awafi da Yin Sa'ayi kuma rashin yin daya daga cikin wadannan yana bata hajji.

Na Farko: Yin Harama: shine Niyyan shiga cikin aikin hajji ko Umurah kuma niyyan takasance a ntareda lokacin da mutum ze cire tufafinsa da talbiyya. Kuma harama tana da nau'o'i uku: Tamattu'I, Qiraani da Ifraadi.

Tamattu'I : ma'anarsa shine musulmi yayi harama da Umara ita kadai a cikin watannain Hajji, idan ya 'isa makka se yayi dawafi yayi sa'ayin umura yayi k'wal kwabo ko saisaye, idan ranar tarwiya wato ranar takwas ga zulhajji, se yayi harama da Hajji shi kad'ai yayi dukkan ayyukan Hajji ya yi hadayan Tamattu'I da yayi idan shi ba mazaunin garin makka ne ba.

Qiiraani: shine yayi harama da Umara da Hajji a tare daga mikaati ko kuma yayi harama da Umara a farko se yashigar da aikin hajji a ciki kafin yayi dawafi kuma ze cigaba da kasancewa a cikin haraminsa har zuwa lokacin da zeyi jifan jamrah a ranar idi se ya aske kansa kuma yayi hadaya kamar me tamattu'i.

Ifraadi : shine yayi harama da hajji kadai, ya cigaba da zama a cikin haraminsa har zuwa lokacin da ze jefi jamrah ranar idi sannan ya aske kansa kuma babu fidya akansa wato babu jini akan haka.