Dasunan Allah mai Rahama mai Jinkai WADANSU ABUBUWA DA'AKA KEBANCE AL'UMMAR MUSULMI DASU AKAN SAURAN AL'UMMU Hakika Allah madaukakin Sarki ya karrama A'ummar musulunci, kuma ya daukakata akan sauran al'ummu, ya kebanceta da wasu abubuwa, ita kadai. Tabbas tasami wannan girmane, saboda daraja da falalan Annabinta Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallam, da imani datayi dashi. Daga cikin daukakashi da Allah yayi bayan yazabeshi daga cikin halittu,ya zaba masa Abokai (wato sahabbai) matemaka agareshi. Allah madaukakain Sarki yace ( "shine wanda yazabeku –sahabbai- kuma be sanya maku wani abu me wahala acikin Addini ba" ) (Sur. Hajji -78.) kuma yace ( "kuma haka muka sanyaku Al'umma mafificiya domin kuzamo masu sheda ga mutane (Annabawan dasuka gabata akan mutanensu) kuma manzo yazama me shesa akanku….") Sur. Baqarah-143). Saboda haka ne yazama dole akan muslmai dasusan abinda suke ciki na ni'ima,da kuma abinda suke akai na alkhairi, don suyi rikoda shi kumasuyi rikodashi kuma suyi aiki domin yadashi……………………….zamu cigaba insha Allah
6 Aug 2007
4 Aug 2007
MATSAYIN SALLAH
at 07:31
23 Jun 2007
BAYANAI GAMEDA SHAFIN
Bismillahir Rahmanir Raheem Muna maku maraba da shigowa wannan Shafi namu na musulunci, wanda zekawo maku, bayanai akan abinda yashafi Rukunnan Musulunci guda biyar, wato Kalmar Tauhidi, Dallah Azumi Zakka da Hajji. Sannan daga baya zamu bayani akan abinda yashafi Mu'amala, kama daga kasuwanci, Hayaa da Auratayya, Zamantakewa da makwabtaka da.......... tareda yin bayani akan Hukunce Hukuncensu a musulunci, tareda kawo dalilai daga cikin Littafin Allah da Sunnar Manzan Allah Sallallahu Alaihi WASAllam, da zantukan dasuka Inganta na Malamai, domin sanarda musulmi wanda yake Bahaushe ko wanda iya karantun Hausa, bayanai masu inganci gameda Addininsa. Sannaan kuma munaso mu dinga kawo maku fatawa ta malamai a cikin gida najeriya ko a wajenta. ALLAH MUKE ROKO DA YAYI MANA JAGORANCI aMIIIIIIIIIIIN.
at 22:55



