ASHURA…… BIKIN SAMUN NASARA AKAN MASU DAGAWA.
Goma ga watan Muharram (Ashura ranace da Allah ya Girmama, kuma Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yayi bikinsa kuma yayi Umarni da Azumtansa, kuma yace gameda Ashura: Ashura wata ranace daga cikin ranakun Allah Madaukakin sarki, kuma wannan rana an kasance ana girmamata a lokacin jahiliyya, kuma yahudawa sun kasance suna daukansa a matsayin Idi, kuma shine Azumi na farko da’aka farlanta akan Musulmi kafin Ramadan.
Imamul Bukhari da Muslim sun ruwaito daga Abdullahi dan Abbas Allah ya k’ara yarda agaresu Yace:- “Yayinda Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasalllam Yazo Madina, ya sama yahudawa suna Azumtan Ranar Ashura, se Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Yace: “Ku bani labarin wannan rana da kuke Azumta, se Sukace: “wannan ran ace me girma Allah ya tseratar da Musa da Mutanensa a cikinta, kuma a cikinta y a halakar da Fir’auna da mutanensa se Annabi Musa yayi Azuminsa , a matsayin godiya ga Allah, saboda haka muma muke Azuminsa, se Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Yace: “To mu mukafi dacewa da Can- Canta da Musa akanku , se Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasllam Ya Azumcesa kuma yayi Umarni da’ayi Azuminsa”
Kuma gameda Falalar Azumin wannan rana Yazo a cikin Hadisi me tsawo cikin Sahihu Muslim daga Abu Qatada Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Yace:- “ kuma Azumin ranar Ashura Ina fatan Allah ya kankare zunuban shekara da ta gabata dashi”
kuma yazo cikin Sahihul Bukhari daga Abdullahi dan Abbas Allah Yakara masa yarda Yace: “Banga MAnzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya kebance wata rana da Azumi kuma yana Fifita Azuminsa akan waninsa ba se Azumin ranar Ashura , da wannan watan wato watan Ramadan.
Kuma sirrin dake cikin Azumin wannan rana shine: Nasara da Allah yabawa Annabi Musa da Mabiynsa da Halakar da Fir’auna da rundunarsa, wato biki ne Goyon baya da Allah yaba Muminai wanda sukayi Annabinsu biyayya kuma suka fita tareda shi domin su kafa wata kasa ta Musulunci sabuwa, kuma farin ciki ne da karya zalunci da dagawa dake tare da Fir’auna da rundunarsa wadandz suka yi dagawa a cikin garin Misra kuma suka yawaita barna a cikinisa.
![](https://blogger.googleusercontent.com/img/b/R29vZ2xl/AVvXsEjb78ZMoOgTRL7G0n2wfKKh2fbTV0b0-1s40upy9CVRz7gdS_MkQZmWHceUmUsW4EZi0DMdCXlB6JzSgyhgh2R-ayVnayTvkkFp8WBvgNZOPE2jndr3Leuja0kXmTCIJ2OluflI-55pCNY/s400/Candles.jpg)
Wannan hoton yanda Shi'a suke kunna kyandura kenan a daren Ashura irin Yanda kiristoci sukeyi.
BIKIN
Amma gameda Ta’aziyyan Shi’a, babu wanda yake jayayya akan Falalan Husaini Allah Yakara yarda agareshi , da Darajojinsa domin ai yana daga cikin Malaman Sahabbai, kuma shugaba ne na Musulmai a duniya da Lahira wadanda aka sansu da Bauta da Jarumtaka da Yalwa… kuma shi d’ane wajen Y’ar mafificin halittu Sallallahu Alaihi Wasallam, itace mafificiya a cikin Y’ayansa, kuma abinda yafaru na kisansa Al’amarine abin k’i mummuna me bak’anta rai a wajen kowani Musulmi, kuma hakika Allah ya dauki fansa daga wanda suka kasheshi, Inda ya wulakantasu a duniya kuma ya sanya su suzama wa’azi, bala’o’I da fitinu suka samesu kuma kad’an ne suka tsira daga cikinsu, kuma me yasa bama ganin shugabanninsu suna zuwa suna Yanka jikinsu kamar yanda sauran mutane keyi ?
Kuma abinda ya kamata a lokacin tunawa da musiban kashe Husaini da makamancinta shine: Hakuri da Yarda da hukuncin Allah da k’addararsa kuma shi Allah yana zab’awa bawansa abinda yafi zama Alkhairi, Sannan Neman Lada wajen Allah madaukakin Sarki sakamakon Hakurin.
Amma be da Kyau ko kad’an abinda muke gani Shi’a na aikatawa na bayyana b’akin ciki da rashin hakuri wanda suka kirkiro kuma suka kallafa ma kansu, Mahaifinsa Aliyyu wanda yafishi Falala shima an kashe shi to meyasa basu rik’I mutuwarsa amatsayin abin ta’aziyya ba? kuma an kashe Usmanu da Umar kuma Abubakar yarasu Allah yakara masu yarda kuma dukkansu sun fishi falala… kuma shugaban Halittu Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallam ya rasu kuma ran mutuwansa ba’ayi abinda yake faruwa ba a ranar Kisan Hussaini, kuma yin bikin Bak’in ciki? Baya cikin Addini kai yafi kama da ayyukan Jahiliyya ( Alfatawa : Vol. 25 p. 307-314, da Iqtida’us siratal mustaqim Vol. 2 p.129 – 131.)
![](https://blogger.googleusercontent.com/img/b/R29vZ2xl/AVvXsEgkOeDcj8bd_efdIs4nJi1HjcUhsLtqO4mIpPhObGWZm6xxC3O3vIe2MRL408tiEFZgFt4iGOmlrgOyWiFU2pue_HHfg8iq67U7mqg3fcrj3um59rh_vcX07nD3yhS8VAtO_k4gIPUk0Ec/s400/Shi'ate+with+blade-1.jpg)
![](https://blogger.googleusercontent.com/img/b/R29vZ2xl/AVvXsEibPVk_pBQ3qH4dpqqXdHO1UIDVZ7CEx1HSvpBWXqksIch-7VZIDanbPMctrSsQMuu0Eu4C6Ero7hTMXVVqEevPNZpkjUujg5efhqrbW-bLaBfHMnjomFfjWhdWuNFyUzmaJ3LqOMdWYJs/s400/Jama'an+shia.jpg)
Wanda ke lura da al’amura ayau ze ga cewa suna kebance ranar Ashura da abubuwa masu yawa:- daga ciki akwai:-
* Azumi munyi bayanin matsayinsa a cikin Shari’ah,
* Akwai raya daren Ashura, da kwad'ayin kuntatama kai wajen yin abinci da yanka iri daban- daban na nama, da bayyanar da Murna da farin ciki.
* Akwai abubuwa dake faruwa a garuruwa daban- daban na ta’aziyya, da bak'in ciki ta hanyar aiwatar da wasu abubuwa na daban kamar yanda Rafidawa (Shia’a) sukeyi da wasunsu.
Yakamata musan matsayin wadannan ayyukan a shari'a, daganan suna iya zama ayyukan neman lada da kusanci zuwa ga Allah, ko kuma sanin rashin shar’antasu, se suzama bidi’ah da zasu nesanta mutum ga Allah.
To dolene mu sani cewa: ayyuka a wajen Allah basa samun karbuwa se sun cika wasu sharudda daga ciki akwai: Me yin aiki ya kasance yana me koyi da Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam, to idan muka duba ayyukan mutane a ranar Ashura sawa’un abubuwanda sukeyi a baya ko a wannan lokaci zamuga cewa suna da Nau’o’I daban daban:
1. akawai abinda yake na bauta : sun ware wwannan rana das wasu bauta na dabam kamar yin tsayuwa cikin daren Ashura, da ziyartan makabartu a cikinsa, da yin sadaka, da bada zakka, da karanta surorin da akwai ambaton Annabi Musa a cikinsu a alfijirin ranar Ashura… wannan da wasunsu, ayi abinda yasaba acikinsu wato dalilin yin aikin shine kebance shi da wani lokaci da Allah be ce a kebance su dayin hakan ba, kuma idan da Allah naso a aikata hakan to da yayi umarni da kwadaitar da yin hakan, kamar yanda ya kwaidaitar da yin Azumi a cikinsa.
To kenan an hana kebance wani lakaci da yin wata ibada ta daban, koda kuwa ace aikin shi karan kansa akwaishi a shar’aih wato ba'a haramtashi ba.
2. abinda yake Al’ada ce ake aikatawa, a ranar Ashura, irin wanda akeyi a Idi daga cikinsu akwai:-
* Yin wanka da sa kwalli da sanya turare da yalwata ma Iyalai a abinci da abin Sha da dafe dafe da toye- toye da yin yanka da bayyana Murna da farin ciki.
* kuma akwai wasu al’adu da suke cike da abin muni, kuma dukkan wadanna abubuwa sun samo asali ne a matsayin mayar da martani ga ta’aziyyan Rafidawa dasuke yi na nuna bakin ciki ga Mutuwan Husaini Allah yakara yarda agareshi, (To se Nasibawa sune wadanda suke nuna k’iyayya ga Ahlul baiti suke kishiyantan Shi’a wato rafidawa, wadanda su kuma suka wuce Iyaka wajen Ahlul baiti) da bayyana zagi garesu da nuna farin ciki, suka kirkiro abubuwan da babu su cikin Addini se suka fad’a cikin kamanceceniya da Yahudawa wajen daukansa a matsayin Idi wato biki kamar yanda ya gabata. (Kamar yanda Shaikhul Islam ya ambata a cikin littafinsa Iqtida’us siratal mustaqim Vol-2 p. 129-134).
* Yin Wanka kuma da sanya kwalli…..babu wani abu acikinsu da ya tabbata.
Imamu Bin Taimiyya yayi nuni ga Hadisan da sukazo dake nuna falalan Ashura yake cewa: dukkaninsu k’arya ce da’akayi wa Manzan Allah, babu wani abu daya inganta a cikinsa in banda Azumi, kuma wannan shine tafarkin Manzan Allah Sallalllahu Alaihi Wasallam.
Allah Madaukakin Sarki yace: "Hakika koyi me kyau ya kasance agareku daga Manzan Allah, ga wanda yake fatan Allah da Rana ta K’arshe kuma ya( ambaci Allah da yawa” Sur. Al-Ahzab -12.
kuma dayawa daga cikin wadannan da suke shagaltuwa da bidi’o’I, dayawa bin ManzanAllah Sallallahu Alaihi Wasallam na wuce su da bin aiki da Sunnarsa.